Wakilin Sin: Dole Ne A Aiwatar Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
Published: 26th, February 2025 GMT
A ranar 25 ga wata ne zaunannen wakilin kasar Sin a majalisar dinkin duniya Fu Cong, ya bayyana a taron kwamitin sulhu na MDD game da batun Isra’ila da Falasdinu cewa, tilas ne a aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a zirin Gaza baki dayanta, don tabbatar da tsagaita wuta mai dorewa. Ya kuma yi kira ga Isra’ila da ta dakatar da aikin soji a yammacin gabar kogin Jordan.
Fu Cong ya bayyana cewa, dole ne mulkin Gaza bayan yakin ya bi ka’idar “Falasdinawa su yi mulkin Falasdinu”, kuma ya kamata kasashen duniya su ba da goyon baya ga sake gina Gaza. Kana kasar Sin ta yi kira ga al’ummomin kasa da kasa da su kara himma wajen kira ga samar da mafita ta siyasa ta kafa kasashe biyu da kuma ba da tabbacin da ya dace da hakan. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
El-rufa’i Ba Zai Halarci Taron Jam’iyyar APC Na Kasa Ba, Kuma Ganduje Na Nan A Shugabanci
A yayin da jam’iyyar APC mai mulki ta shirya taron kwamitin zartaswa na kasa wanda ake sa ran za ta yi ranar Laraba, jam’iyyar ta musanta rade-radin da ake yi na cewa shugaba Bola Tinubu na iya neman shugaban jam’iyyar, Dakta Abdullahi Ganduje, ya sauka daga mukaminsa. Sakataren jam’iyyar na kasa, Sanata Ajibola Basiru, ya karyata jita-jitar a wata hira da aka yi da shi, inda ya jaddada cewa, jam’iyyar ta saba gudanar da irin wannan taron, ba wai sai don shirin zabe ba. Amurka Za Ta Illata Kanta Bisa Tsara Matakan Kayyade Samar Wa Sin Sassan Na’urorin Laturoni Na Semiconductor Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa A halin da ake ciki, tsohon gwamnan jihar Kaduna kuma tsohon ministan birnin tarayya, Nasir El-Rufai, ya tabbatar da cewa ba zai halarci taron jam’iyyar na kasa ba a yayin da yake magana a shirin ‘PrimeTime’ na Arise Television a daren ranar Litinin, inda ya bayyana rashin sanar da shi a matsayin dalilin rashin halartarsa. “Ba zan samu halartar taron kolin jam’iyyar APC na kasa ba. Zan koma birnin Alkahira, inda nake shafe yawancin lokaci na. Ban sami isasshiyar sanarwa ba. Kundin tsarin mulkin jam’iyyarmu ya bayar da kwanaki 21, ko kuma kwanaki 14 don samun sanarwar gudanar da irin wannan taron. Ba na tsammanin an turo min da gayyatar,” in ji shi. Ya ci gaba da bayyana cewa, “Idan ya kasance, ban samu gayyatar makonni biyu zuwa makonni uku da suka gabata ba. Don haka, ina da tsare-tsare na, kuma gobe zan tafi. Amma abokaina da yawa za su halarta, don haka ba zan rasa kome ba. Zan san abin da aka tattauna.” Babban taron dai, zai kasance karkashin jagorancin shugaba Tinubu, inda ake sa ran mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari za su halarta. Haka kuma akwai shugaban majalisar dattawa Dr. Godswill Akpabio, gwamnonin jam’iyyar APC na baya da na yanzu, tsoffin shugabannin majalisar wakilai da masu rike da madafun iko, shugabannin jam’iyyar na jihohi, kwamitin ayyuka na kasa, da sauran masu ruwa da tsaki.Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp