Leadership News Hausa:
2025-03-29@05:17:35 GMT

Mugunta Fitsarin Fako…

Published: 26th, February 2025 GMT

Mugunta Fitsarin Fako…

Shugaban kungiyar masu masana’antun ta Amurka, Jay Timmons ya ce, manufar ta kasance babban kalubale ga masana’antun kasar, domin ta haifar da rashin tabbas, da wargaza tsara yadda ’yan kasuwa za su tafiyar da kasuwancinsu da kuma saka hannun jari a nan gaba.

Kazalika, wani babban masanin tattalin arziki a Cibiyar Nazarin Tsara Manufofin Tattalin Arziki dake Amurka, Dr.

Robert Scott ya ce, manufar ‘Amurka ta Zamanto Farko’ ta kasance bala’i ga ma’aikatan Amurka” domin tana “haifar da asarar aiki, da rage albashi, da rage damammakin ci gaban tattalin arziki ga ma’aikatan Amurka.”

Bayanan wadannan masu ruwa da tsaki sun nuna yadda manufar take shafar Amurkar ciki da waje, kuma dama kasashen duniya musamman kasar Sin sun gargadi kasar cewa, abin ba zai haifar wa hatta ita kanta Amurkar da wani kyakkyawan sakamako ba illa tayar da zaune tsaye.

Bugu da kari, yayin da Amurka ta zabi tafiyar da huldodinta na tattalin arzikin duniya cikin sarkakiya, masu iya magana sun ce, “idan za ka gina ramin mugunta, to gina shi gajere don watakila kai za ka fada”, sannan “Mugunta fitsarin fako, tana komawa ga mai yi!”(Abdulrazaq Yahuza)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Za Ta Dauki Matakai Don Kiyaye Hakki Da Muradun Kamfanoninta

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya ce kasar Amurka ta yi amfani da batun kayayyakin da ake fitarwa zuwa kasashen waje, kamar jerin sunayen kamfanoni, wajen sanyawa sauran sassa takunkumai bisa hujjar “barazana ga tsaron kasa, da kuma keta manufofin diplomassiyar Amurka”, wanda hakan ya zama wani babban mataki na nuna fin karfi.

Guo ya bayyana hakan ne yayin da ya jagoranci taron manema labarai na yau da kullum na yau Laraba, lokacin da yake tsokaci game da matakin Amurka na shigar da kamfanonin Sin fiye da goma, cikin jerin sunayen wadanda ta hana su shigar da hajoji Amurka, bisa jadawalin da ma’aikatar kasuwancin Amurka ta fitar. Game da hakan, Guo ya ce bangaren Sin zai dauki matakai don kiyaye hakki da muradun kamfanonin kasar Sin.

Kwalara Ta Kashe Mutum 14, Ana Zargin 886 Sun Kamu A Nijeriya – NCDC ‘Yan ta’adda Sun Kai Hari Sansanin Sojoji, Sun Kashe Uku A Borno

Dangane da rahoton da Amurka ta fitar game da “ka’idar barazana ta kasar Sin”, Guo Jiakun ya ce, Sin na shawartar Amurka da ta daina kallon dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka da tsohon tunanin yakin cacar baka, ta kuma daina yada kalaman nan na “barazanar kasar Sin”.

Game da tattalin arzikin Asiya kuwa, Guo Jiakun ya ce, kasar Sin za ta sa kaimi ga samun ci gaba mai inganci, da bude kofa ga kasashen waje, da yin hadin gwiwa da sauran kasashen Asiya, wajen ba da sabbin gundumawa, don inganta ci gaban tattalin arzikin duniya. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Ta’addancin sojojin Amurka a kan Yemen ‘barazana’ ne ga zaman lafiyar duniya
  • Taron Boao Ya Sake Ba Duniya Damar Ganin Abubuwa Masu Jan Hankali Game Da Sin
  • Xi Jinping Ya Gana Da Wakilan Masana’antu Da Cinikayya Na Kasa Da Kasa
  • Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba
  • Jagora Ya Yi Kira Ga Iraniyawa Su Fito Don Gudanar Da Gagarumar Zanga-Zargar Ranar Kudus Ta Duniya
  • Iran Ta Bada Amsa Ga Wasikar Shugaban Kasar Amurka Ta Gayyatar Kasar Zuwa Tattaunawa Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya
  • Kasar Sin Na Adawa Da Kara Yawan Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Amurka Ta Takaita Fitar Da Kayayyakinsu
  • Karin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arzikin Duniya
  • Ranar Quds : Hamas ta bukaci masu huduba su sadaukar da jawabansu kan Falastinu
  • Sin Za Ta Dauki Matakai Don Kiyaye Hakki Da Muradun Kamfanoninta