Leadership News Hausa:
2025-04-19@13:08:28 GMT

Mugunta Fitsarin Fako…

Published: 26th, February 2025 GMT

Mugunta Fitsarin Fako…

Shugaban kungiyar masu masana’antun ta Amurka, Jay Timmons ya ce, manufar ta kasance babban kalubale ga masana’antun kasar, domin ta haifar da rashin tabbas, da wargaza tsara yadda ’yan kasuwa za su tafiyar da kasuwancinsu da kuma saka hannun jari a nan gaba.

Kazalika, wani babban masanin tattalin arziki a Cibiyar Nazarin Tsara Manufofin Tattalin Arziki dake Amurka, Dr.

Robert Scott ya ce, manufar ‘Amurka ta Zamanto Farko’ ta kasance bala’i ga ma’aikatan Amurka” domin tana “haifar da asarar aiki, da rage albashi, da rage damammakin ci gaban tattalin arziki ga ma’aikatan Amurka.”

Bayanan wadannan masu ruwa da tsaki sun nuna yadda manufar take shafar Amurkar ciki da waje, kuma dama kasashen duniya musamman kasar Sin sun gargadi kasar cewa, abin ba zai haifar wa hatta ita kanta Amurkar da wani kyakkyawan sakamako ba illa tayar da zaune tsaye.

Bugu da kari, yayin da Amurka ta zabi tafiyar da huldodinta na tattalin arzikin duniya cikin sarkakiya, masu iya magana sun ce, “idan za ka gina ramin mugunta, to gina shi gajere don watakila kai za ka fada”, sannan “Mugunta fitsarin fako, tana komawa ga mai yi!”(Abdulrazaq Yahuza)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Masu garkuwa za su mutu ta hanyar rataya a Edo – Okepebolo

Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo ya bayyana cewa masu garkuwa da mutane da aka samu da laifi a jihar za su fuskanci hukuncin kisa ta hanyar rataya.

Okpebholo ya bada tabbacin a shirye yake ya sanya hannu akan sammacin kisa na waɗanda aka yankewa hukunci a jihar idan kotu ta same su da laifi.

An tsinci gawar mabaraci mai shekara 75 a Neja PDP ba ta shirya yin zaɓen 2027 ba – Wike

Gwamna Okpebholo ya bayyana hakan ne a wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a garin Uromi, inda ya tattauna da shugabanni da ’yan uwa na yankin unguwar ’yan Arewa mazauna Esan.

“Ku tuna cewa Majalisar Dokokin Jihar Edo (EDHA) ta zartar da wani ƙudiri na gyara dokar hana garkuwa da mutane (da wasu dokoki da suke da alaƙa da na shekarar 2013)”.

Ƙudirin dokar ya tanadi hukuncin kisa ga masu garkuwa da mutane sannan kuma ya ba da umarnin ƙwacewa da rushe dukiyoyin da ake yin amfani da su wajen aikata laifukan.

A cewar gwamnan, gwamnatinsa ba za ta lamunci rashin tsaro, kisan gilla da kuma garkuwa da mutane ba.

“Na ɗauki batun rashin tsaro da muhimmanci kuma ba zan karkatar da ƙa’idar ba sai dai a yi amfani da su sosai, sabuwar dokar jihar ta ba mu damar rusa kadarorinsu da ƙwace musu filayensu.

“Za mu kawo masu garkuwa da mutane a gaban jama’a, mu kashe su domin mu nuna muhimmancinmu a kan dokokin da Majalisar Edo ta riga ta yi, ba zan ji tsoron sanya hannu a kai ba,” in ji shi.

Gwamnan ya yi kira ga kowa da kowa da su ba gwamnatinsa haɗin kai don tabbatar da tsaron jihar, yana mai cewa “tsaro aikin kowa ne ba na hukumomin tsaro kaɗai ba”.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • China Na Neman Ƙasashe Su  Haɗe Wa Amurka Kai Sakamakon Ƙarin Haraji
  • Amurka ta sanar da cewa za ta rage yawan sojojinta a Syria da rabi
  • Masu garkuwa za su mutu ta hanyar rataya a Edo – Okepebolo
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Harin Amurka Na Jiya A Yemen Ya Kai 74
  • Amurka Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadancinta Kimani 30 A Duniya
  • Alkaluman Tattalin Arzikin Sin Sun Shaida Dorewar Ingancin Tattalin Arzikinta
  • Kare-karen Harajin Amurka “Dara Ta Ci Gida”
  • WTO Ta Yi Gargadi Akan Karin Kudin Fito Na Amurka
  • Batawa Sin Suna Ba Zai Taimaka Kawar Da Tambarin Amurka A Matsayin Daular Kutsen Intanet Ba
  • Mizanin Hada-hadar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 5.4% A Rubu’in Farko Na Bana