An shawarci majalisar dokokin kasar da su mai da hankali kan ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin kasar nan domin inganta shugabanci nagari.

Masu kiran waya a shirin “KAKAKI” na gidan Rediyon Najeriya Karama FM ne suka bada shawarar hakan a lokacin da suke ba da tasu gudunmawar a kan batutuwan da suka shafi kasa.

Sun bayyana damuwarsu kan rahotannin karar da wata sanata daga jihar Kogi, Natasha Akpoti, ta shigar kan shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, biyo bayan  zargin bata suna.

Alhaji Ibrahim Alaramma, Idris Adamu Danfulani, da Sani Batira sun jaddada bukatar shugabannin majalisar su tabbatar da kafa doka mai inganci don yaki da talauci da rashin tsaro.

Shi ma da yake jawabi, wani bako a shirin, Alhaji Suleiman Muhammad ya yi kira ga gwamnati da ta kara samar da ayyukan raya kasa da ababen more rayuwa kamar yadda ake yi a kasashen da suka ci gaba.

 

Suleiman Kaura

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tawagar Aikin Ceto Ta Kasa Da Kasa Ta Kasar Sin Ta Isa Myanmar

A cewar hukumar raya kasashe ta kasar Sin, kashin farko na kayayyakin ya hada da tantuna da barguna da kayayyakin lafiya. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gangamin da zan yi a mazaɓata babu fashi — Natasha
  • Ana Zaman Dar-dar A Kasar Zimbabwe Saboda Shirin Zanga-zangar Tsofaffin Sojaji
  • Sanata Yari Zai Tallafa Wa Marayu 20,000 A Zamfara
  • Kasar Sin Ta Nanata Adawa Da Matakan Tilastawa Da Nuna Babakeren Tattalin Arziki
  • Tawagar Aikin Ceto Ta Kasa Da Kasa Ta Kasar Sin Ta Isa Myanmar
  • Muna so a nuna wa duniya mutanen da suka kashe ’yan Arewa a Edo — Gwamnan Kano
  • Sani Ahmad Lere Na Radio Nijeriya Kaduna Ya Zama Falakin Lere
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Girgizar Kasa: Shugaban Kasar Myanmar Ya Mika Godiya Ga Tawagar Likitocin Yunnan Ta Kasar Sin
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Fiji: Ya Kamata A Koyi Fasahohin Da Kasar Sin Ta Samu A Fannin Raya Kasa