Kungiyar Hamas wacce take iko da Zirin Gaza ta bada sanarwan cewa an kawo karshen takaddama da HKI dangane da jinkirin da tayi wajen sakin fursinonin Falasdinawa 620 a ranar Asabar da ta gabata bayan da ta saki fursinoni yahudawa har 6.

Tashar talabijin ta Prersstv a nan Tehran ta nakalto kakakin kungiyar Hazem Qassem yana fadar haka a yau Laraba, ya kuma kara da cewa, gwamnatin kasar Masar ce mai shiga tsakani, kuma ta lamuncewa kungiyar kan cewa shirin musayar zai sake komawa kan yadda aka tsara shi, sannan HKI zata sake wadannan fursinoni Falasdinawa.

Banda haka labarin ya kara da cewa a gobe Alhamis ma kungiyar Hamas zata mika gawakin yahudawa 4 wadanda take tsare da su a hannunta tun cikin yakin tufanul Aksa.

A Zagaye na farko na musayar fursinonin tsakanin Hamas da HKI dai, Hamas ta sake yahudawa 33, a yayinda yahudawan suka saki fursinoni falasdinawa kimani 2000.

Marhala ta karshe bayan musayar fursinoni da gawawwaki shi ne, janyewar sojojin HKI daga zirin gaza, ko yankin philidelpia  da kuma maganar sake gina gaza. Bayan da HKI ta rusa gine-gine har 170,000 a cikin shekara guda da watanni 3.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 An Yi Ganawa A Tsakanin Ammar Hakim Na Iraki Da Shugaban Kasar Masar Abdufttah Al-Sisi

Shugaban kungiyar ‘al-Hikimah” na kasar Iraki Ammar Hakim ya gana da shugaban kasar Masar Abdulfattah al-sisi. A yayin ganawar  Ammar Hakim ya jaddada muhimmancin taimaka wa kokarin da Masar take yi na ganin an hana korar falasdinawa daga yankunansu zuwa wajen Falasdinu.

Ammar Hakim ya kuma ce, a yayin wannan ganawar na bayyana wa shugaban kasar jinjinawarmu akan yadda Masar ta kasance mai taimaka wa Falasdinawa.”

Haka nan kuma mun nuna goyon bayanmu ga kokarin Masar al’umma da gwamnati na hana tilasatawa Falasdinawa yin hijira da kuma kare hakkokin Falasdinawa da riko da kasarsu.

Har ila yau Ammar Hakim ya ce ganawar tasu ta tabo batutuwa da su ka shafi halin da ake ciki a wannan yankin da kuma wajabcin aiki a tsagaita wutar yaki a yankin Gaza.

Sayyid Ammar Hakim ya kuma yi ishara da muhimmanci sake gina yankin na Gaza ba tare da an fitar da mazaunansa daga ciki ba. Bugu da kari bangarorin biyu sun jaddada muhimmanci kafawa Falasdinawa daularsu akan iyakokin 1967 da birnin Kudus zai zama babban birninta domin haka ne hanyar samar da zaman lafiya a cikin wannan yankin.

Akan halin da ake ciki a matakin wannan yankin kuwa, Sayyid Ammar Hakim ya ce; Kasar Iraki tana son ganin an sami zaman lafiya a cikin wannan yankin da kuma warware sabanin da ake ciki a wannan yankin da kusanto da fahimtar juna a tsanakin bangarori mabanbanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ukraine ta cimma yarjejeniya da Amurka kan haƙar ma’adinai
  • Jami’an Diblomasiyyar Kasashen Rasha Da Amurka Zasu Sake Haduwa A Birnin Istambul A Gobe
  • An Cimma Matsaya Kan Sakin Fursunonin Falasdinawa 206 Da Isra’ila Ta Jinkirta
  • Hamas ta yi tir da matakin Isra’ila na shirin takura masu ibada a masallacin Quds
  •  HKI: Hamas Ta Sake Gina Kanta A Arewacin Gaza
  •  An Yi Ganawa A Tsakanin Ammar Hakim Na Iraki Da Shugaban Kasar Masar Abdufttah Al-Sisi
  • Dan kwallon Najeriya ya mutu bayan fadowa daga bene a Uganda
  • Kungiyar Hamas Ta Dakatar Da Tattaunawa Da HKI Har Zuwa Sakin Fursinoni Falasdinawa
  • Hamas ta yaba da irin goyon bayan da Sayyed Nasrallah ya baiwa Falasdinu