Kungiyar Hamas wacce take iko da Zirin Gaza ta bada sanarwan cewa an kawo karshen takaddama da HKI dangane da jinkirin da tayi wajen sakin fursinonin Falasdinawa 620 a ranar Asabar da ta gabata bayan da ta saki fursinoni yahudawa har 6.

Tashar talabijin ta Prersstv a nan Tehran ta nakalto kakakin kungiyar Hazem Qassem yana fadar haka a yau Laraba, ya kuma kara da cewa, gwamnatin kasar Masar ce mai shiga tsakani, kuma ta lamuncewa kungiyar kan cewa shirin musayar zai sake komawa kan yadda aka tsara shi, sannan HKI zata sake wadannan fursinoni Falasdinawa.

Banda haka labarin ya kara da cewa a gobe Alhamis ma kungiyar Hamas zata mika gawakin yahudawa 4 wadanda take tsare da su a hannunta tun cikin yakin tufanul Aksa.

A Zagaye na farko na musayar fursinonin tsakanin Hamas da HKI dai, Hamas ta sake yahudawa 33, a yayinda yahudawan suka saki fursinoni falasdinawa kimani 2000.

Marhala ta karshe bayan musayar fursinoni da gawawwaki shi ne, janyewar sojojin HKI daga zirin gaza, ko yankin philidelpia  da kuma maganar sake gina gaza. Bayan da HKI ta rusa gine-gine har 170,000 a cikin shekara guda da watanni 3.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Gudanar Da Harkokin Cudanya Da Musayar Al’adu Tsakanin Sin Da Malaysia A Birnin Kuala Lumpur 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Ta Sake Aiwatar Da Kisan Kiyashi A Sansanin Falasdinawa Na Jabaliya
  • Hamas ta gabatar da shawara kan yarjejeniyar musayar fursunoni da tsagaita wuta
  • ’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista
  • Kasar Pakistan Ta Kara Jaddada Dokar Rashin Amincewa Da HKI A Matsayi Kasa
  • An Kashe Shanu 36, an ba 42 guba a Filato
  • Araghchi: babu tattaunawa kan batun tace sinadarin uranium
  • An Gudanar Da Harkokin Cudanya Da Musayar Al’adu Tsakanin Sin Da Malaysia A Birnin Kuala Lumpur 
  • Hamas Ta Fadawa Iyalan Yahudawan Da Take Tsare Dasu A Gaza Kan Cewa ‘Ya’yansu Zasu Koma A Cikin Akwatunan Gawaki
  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Shirin Sakin Dukkanin Fursunonin Isra’ila Bisa Sharuddan Da Ta Gindaya
  • Gwamnatin Kano Za Ta Sake Buɗe Makarantun Kwana 10 Don Inganta Ilimin Yara Mata