Sheikh Na’im Kasim Ya Gana Da Ministan Harkokin wajen Kasar Iran Da Shugaban Majalisar Dokoki
Published: 26th, February 2025 GMT
Babban sakataren kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Kasim ya gana da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Arigchi da kuma shugaban majalisar dokokin kasar Iran Muhammad Bakir Qalibof a birnin Beirut babban birnin kasar Lebanon.
Tashar talabijan ta Almayadeen ta kasar Lebanon ta bayyana cewa Jami’an gwomnatin 2 sun je kasar Lebanon ne don halattan taron Jana’izar manya-manyan shahidan kungiyar kuma shuwagabannin kungiyar, Shahid Sayid Hassan Nasarallah, da kuma magajinsa Sayid Hashin Safiyyuddeen.
Labarin ya kara da cewa jakadan kasar Iran a Lebanon Mujtaba Amani ya sami halattan taron inda bangarorin suka tattauna sabbin al-amura da suke tasowa a kasar da kuma yankin kudancin Asiya da kuma al-amura da suke faruwa a duniya gaba daya.
A cikin jawabin da ya gabatar a taron jana’izar dai, sheikh Qasim ya bayyana cewa kungiyar Hizbullah zata ci gaba a kan tafarkin Shahid Hassan Nasaralla. Sannan al-amura da dama sun sauya, don haka zasu yi aikin bisa abinda suka ga ya dace a ko wani lokaci.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Gudanar Da Taron Kasa da Kasa Don Tallafawa Yan Gudun Hijirar A Sudan
Jami’an diblomasiyya daga kasashen duniya da dama, da kuma wakilan kungiyoyin agaji daban-daban sun hadu a birnin London na kasar Burtania don tattauna batun yakin da ke faruwa a kasar Sudan wanda a halin yanzu yake cika shekaru 2 ke nan.
Shafin yanar gizo na labarai ‘Afrika New” ya bayyana cewa, taron na kwana guda ya tattara wakilai daga kasashen Faransa, Burtaniya, Jamus da kuma kungiyar tarayyar Turai, har’ila yau da kasashen da suke makobtaka da kasar ta Sudan.
Labarin ya kara da cewa, yakin na Sudan wanda yake cika shekaru biyu, ya zuwa yanzu ya lakume rayukan mutane akalla 20,000, sannan ya yi sanadiyar kauracewar mutane kimani miliyon 14 zuwa cikin kasar da kuma kasashe makobta, sannan wasu da dama ji raunuka.
Ministan harkokin wajen kasar Burtania David Lammy, a jawabin da ya gabatar a taron na ranar Talaya ya bayyana cewa za’a dauki lokaci kafin a dawo da zaman lafiya a kasar ta sudan, Amma abunda wannan taron yake nema shi ne samun wata kafa ta isar da kayakan agaji ga wadanda suke tsananin bukatarsu a yankuna daban daban na kasar da kasashe makobta.