Babban sakataren kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Kasim ya gana da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Arigchi da kuma shugaban majalisar dokokin kasar Iran Muhammad Bakir Qalibof a birnin Beirut babban birnin kasar Lebanon.

Tashar talabijan ta Almayadeen ta kasar Lebanon ta bayyana cewa Jami’an gwomnatin 2 sun je kasar Lebanon ne don halattan taron Jana’izar manya-manyan shahidan kungiyar kuma shuwagabannin kungiyar, Shahid Sayid Hassan Nasarallah, da kuma magajinsa Sayid Hashin Safiyyuddeen.

Wadanda sojojin HKI suka kashe ko suka kaisu ga shahada a shekarar da ta gabata.

Labarin ya kara da cewa jakadan kasar Iran a Lebanon Mujtaba Amani ya sami halattan taron inda bangarorin suka tattauna sabbin al-amura da suke tasowa a kasar da kuma yankin kudancin Asiya da kuma al-amura da suke faruwa a duniya gaba daya.

A cikin jawabin da ya gabatar a taron jana’izar dai,  sheikh Qasim ya bayyana cewa kungiyar Hizbullah zata ci gaba a kan tafarkin Shahid Hassan Nasaralla. Sannan al-amura da dama sun sauya, don haka zasu yi aikin bisa abinda suka ga ya dace a ko wani lokaci.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Sin da Afirka ta Kudu sun kara zurfafa alakar da ke tsakanin juna

A yayin taron ministocin harkokin wajen kasashen G20 da aka yi a birnin Johannesburg, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi da takwaransa na Afirka ta Kudu Ronald Lamola sun yi wata ganawa ta musamman, inda suka tattauna dangantakar kasashensu da manufofinsu.

Sun amince da manufa guda don habaka tasirin Duniya, da nufin tabbatar da ingantacciyar murya guda ta kasashe masu tasowa.

Wang ya bayyana a yayin taronsu cewa, kasar Sin a shirye take ta kara karfafa hadin gwiwar cin moriyar juna tsakaninta da kasar Afirka ta kudu, da kara gaggauta bunkasuwar kasashen biyu, da kuma kara yin hadin gwiwa don kara daukaka murya da wakilci na kasashe masu tasowa, musamman kasashen Afirka a cikin ajandar kasa da kasa.

Wannan tattaunawar ta faru ne a wani muhimmin lokaci a yayin da ake gudanar da taron ministocin harkokin wajen kasashen G20 a birnin Johannesburg  na Afirka ta kudu, inda aka baiwa kasashen biyu damar karfafa kawance da ba da shawarar yin tasiri a shawarwari na kasa da kasa.

All Posts

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugabannin APC sun gana gabanin babban taron jam’iyyar na ƙasa
  • El-rufa’i Ba Zai Halarci Taron Jam’iyyar APC Na Kasa Ba, Kuma Ganduje Na Nan A Shugabanci 
  • Nebenzia : Hare-haren Sojojin Isra’ila a Lebanon da Syria na kara dagula lamura a yankin
  • Ministan Harkokin Wajen Rasha Ya Fara Ziyarar Aiki A Nan Tehran
  • IRGC Ta Bayyana Cewa Taron Jana’izar Nasarallah Ya Yi Tisara A Duniya Gaba Daya Saboda Barazanar Da Jiragen Yakin HKI Ta Yi Wa taron
  • Iran ta yi Allah wadai da keta hurumin kasar Lebanon da Isra’ila ta yi
  • Kasashen Sin da Afirka ta Kudu sun kara zurfafa alakar da ke tsakanin juna
  • Pezeshkian: Hizbollah tana nan a raye a kan tafarkin gwagwarmaya
  • Tawagar Iran a Beirut ta gana da shugabannin Lebanon