HausaTv:
2025-03-29@02:58:31 GMT

Sojojin Iran Sun Kammala Atisayen Zulfikar 1403 Da Faretin Sojojin Ruwa

Published: 26th, February 2025 GMT

Sojojin kasar Iran sun kammala atisayen hadin giuwa mai suna Zolfaghar 1403 a jiya Talata tare da faretin sojojin Ruwa na kasar.

Atisayen ya hada sojojin sama da na ruwa ne, saboda jarraba yadda bangarorin biyu zasu yi aiki tare a lokacin yaki, duk da cewa ko wani bangare yana aiki a inda ya kore, ya ke kuma da masaniya a kansa.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa, sojojin zasu hada kai don tabbatar da zaman lafiya a yankin Asiya ta kudu cikin ruwa da kan tudu tare.

Manya-manyan kwamandojin sojojin kasar wadanda suka hada da Rear Admiral Habibollah Sayyari mataimakin babban kwamnadan sojojin kasar a bangaren tsare-tsare. Da kuma Manjo Janar Abdulrahim Musavi babban kwamandan sojojin kasar iran.

Atisayen ya hada rawar daji a karkashin ruwa don gwada aiki da makamai, da kuma tudun ruwa shi ma don gwada makaman da ake da su. Sannan da yadda za’a yi rundunonin su yi aiki tare, idan bukatar haka ta taso.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sojojin kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kaduna Ta Jadadda Kudurin Ta Wajen Samarda Tsaftatacen Ruwan Sha Ga Al’umma 

 

Ma’aikatar Ayyuka da Samar da Kayayyakin More Rayuwa, tare da hadin gwiwar First Impression Communication Limited, ta shirya wani taro kan shirin Samar da Ruwa Mai Tsafta a Birane da Karkara da Tsabtace Muhalli da Kiwon Lafiya (SURWASH) da ya gudana a Arewa House, a Kaduna.

 

Da yake bude taron, Kwamishinan Ayyuka da Samar da Kayayyakin More Rayuwa, Dakta Ibrahim Hamza, ya jaddada aniyar gwamnatin jihar na magance matsalar karancin ruwa a jihar.

 

Kwamshinan wanda Mataimakin Daraktan Albarkatun Ruwa, David Roven Aliyu ya wakilta, ya bayyana kokarin da gwamnati ke yi, ciki har da gina rijiyoyin burtsatse a wasu al’ummomi domin inganta tsaftar muhalli da kiwon lafiya.

 

“Shirin SURWASH na Najeriya wani shiri ne da Asusun Bada Lamuni na Duniya (World Bank) ke daukar nauyinsa da dala miliyan 700 domin inganta ayyukan WASH a jihohi bakwai na Najeriya, ciki har da Kaduna.

 

Manufar shirin ita ce samar da ruwan sha mai tsafta ga mutane miliyan shida da kuma inganta tsaftar muhalli ga mutane miliyan 1.4.

Dakta Hamza ya bayyana cewa an ware kananan hukumomi guda shida a Jihar Kaduna wanda suka hada da —Soba, Igabi, Chikun, Jaba, Jema’a, da Sabon Gari—domin tabbatar da su sun samu tsaftatacen Ruwa Sha a yankunan su.

 

“Da zarar wadannan yankuna sun cika ka’idojin da ake bukata, za a kara zabar karin kananan hukumomi guda bakwai domin shirin,” in ji shi.

 

Ya bukaci jama’a su kare kayayyakin tsafta da kiwon lafiya da gwamnati ta samar domin su dade ana amfana da su.

 

A nasa jawabin, Shugaban Shirin SURWASH na Kaduna, Mista Esau Ambinjah, ya jaddada muhimmancin hadin gwiwar al’umma wajen kare rijiyoyin burtsatse da sauran kayayyakin tsafta.

 

Ya kuma bayyana cewa an riga an zabi kananan hukumomi guda bakwai—Sanga, Makarfi, Kudan, Zaria, Kaduna ta Arewa, Kaduna ta Kudu, da Zangon Kataf—domin shirin SURWASH.

 

A nata jawabin, Shugabar Kungiyar Mata Musulmi ta Najeriya (FOMWAN), Amira Hafsatu Musa Isa, ta bada shawarar cewa ya kamata a sanya abun da ya dace da al’adu da addini a cikin shirye-shiryen wayar da kai.

 

Haka kuma, Shugabar Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen mata a Kaduna, Bishop Eister Yawai, ta bukaci a fadada yakin wayar da kan SURWASH zuwa wuraren addinai.

 

Ta bayyana cewa samun tsaftataccen ruwa yana da matukar muhimmanci wajen hana yaduwar cututtukan da ke da nasaba da ruwa.

 

Ta kuma bukaci gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki su kara kaimi wajen magance matsalar karancin ruwa a wasu al’umomi.

 

Wanda ya gabatar da shirin, Yusuf Idris, ya gabatar da sanarwar wayar da kai na SURWASH da aka fassara cikin Hausa da turanci, inda mahalarta suka gabatar da ra’ayoyinsu domin inganta shirin.

 

Cov/Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kaduna Ta Jadadda Kudurin Ta Wajen Samarda Tsaftatacen Ruwan Sha Ga Al’umma 
  • Iran: Ta’addancin sojojin Amurka a kan Yemen ‘barazana’ ne ga zaman lafiyar duniya
  • Iran Ta Gudanar Da Faretin Jiragen Ruwa A Tekun Farisa Da Kuma Tekun Caspian Don Raya Ranar Kudud Ta Duniya
  • Sojojin Sudan Suna Ci Gaba Da Samun Nasara A Akan Dakarun Kai Daukin Gaggawa
  •  Sojojin Iran: Gwagwarmaya Ce Kadai Hanyar Warware Matsalar Falasdinu
  • Iran, Lebanon, Iraki, Yemen sun fara atisayen hadin gwiwa na goyan bayan Gaza
  • Kwara Ta Gargadi Jama’a Akan Gine-Gine Akan Bututun Ruwa
  • HKI Ta Kai Hare-hare A Falasdinu Da Kasar Lebanon
  •  Sojojin Sudan Sun Kwace Wuri Na Karshe Da Yake A Hannun “Rundunar Kai Daukin Gaggawa” A Cikin Birnin Khartum
  • Yadda Binciken Kayan Tarihi Ke Zakulo Asalin Magabata Da Wayewar Kansu A Kasar Sin