Jami’an diblomasiyyar kasashen Rasha da Amurka zasu sake haduwa a gobe Alhamis 27 ga watan Fabarayru a birnin Istambul na kasar Turkiyya.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Lavrov yana fadar haka a kasar Qatar, ya kuma kara da cewa a haduwarsu na gobe kasashen biyu zasu maida hankali ne wajen sake bude ofisoshin jakadancin kasashen biyu a kasashensu.

Ministan ya kara da cewa, dangantaka tsakanin Rasha da Amurka bai taba yin kyau ba tun lokacin tarayyar Soviet, amma ta dan kyautata a lokacin shugabancin Trump na farko.  Sannan bayan sake dawowan Trump da alamun dangantakar zata yi kyau.

A gobe Alhamis dai bangarorin biyu zasu dubu abubuwan da suke hana ruwa guda a ofisoshin jakadancin kasashen biyu a Washington da Mosco.

A ranar 18 ga watan Fabrayrun shekara ta 2025 ne a karon farko tun bayan fara yakin Ukraine jami’an diblomasiyyar kasashen biyu suka hadu a birnin Riyad na kasar Saudiya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Rasha Da Ukraine Sun Amince Da Tsagaita Wuta A Tekun Black Sea

Fadar Gidan Gwamnatin Amurka (WhiteHouse), ta ce Rasha da Ukraine sun amincewa Jiragen jigilar kayayyakin kasuwanci gudanar da zirga-zirga cikin aminci a tekun Black Sea ba tare da kai musu hare-haren soji ba. Amurka ta fitar da wannan sanarwar ne bayan jami’an Amurka sun gana da wakilan kasashen biyu a Saudiyya a ranar Talata. Dole Ne A Tauna Tsakuwa Don Aya Ta Ji Tsoro Sin Na Ci Gaba Da Kasancewa Cibiyar Rarraba Hajojin Da Masana’antu Ke Sarrafawa Sai dai Rasha ta ce, dole ne a dage wasu takunkuman da aka sanya wa bankuna, kamfanonin inshora, da masu fitar da abinci, kafin yarjejeniyar tsagaita bude wutar ta fara aiki. Sai dai, Shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya zargi Rasha da “kwarara karya” game da sharuddan yarjejeniyar. Rahotanni sun ce shugaban Amurka Donald Trump na ganawa da jakadun Amurka a fadar White House kan lamarin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron Boao Ya Sake Ba Duniya Damar Ganin Abubuwa Masu Jan Hankali Game Da Sin
  • Tinubu zai sake zama shugaban ƙasa a 2027 — Akpabio
  • Jerin Gwanon Ranar Kudus Na Ci Gaba Da Gudana A Kasashen Duniya
  • Kasar Sin Na Adawa Da Kara Yawan Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Amurka Ta Takaita Fitar Da Kayayyakinsu
  •  Kasashen Iran Da Katar Sun Jaddada Muhimmancin Shigar Da Dukkanin Bangarorin  Al’ummar Kasar A Cikin  Sha’anin Kasar
  • Ranar Kudus: al’ummar Iran zasu nuna hadin kan su ga duniya_ Pezeshkian
  • Sudan : Janar al-Burhan Ya Shelanta ‘yantar Da Birnin Khartoum
  • Sin Za Ta Dauki Matakai Don Kiyaye Hakki Da Muradun Kamfanoninta
  • Rasha Da Ukraine Sun Amince Da Tsagaita Wuta A Tekun Black Sea
  • Araqchi: Har yanzu Iran ba ta mayar da amsa ga wasikar Trump kan tattaunawar nukiliya ba