Leadership News Hausa:
2025-04-18@23:16:42 GMT

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Taimakon Soji Da Amurka Ke Bai Wa Taiwan

Published: 27th, February 2025 GMT

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Taimakon Soji Da Amurka Ke Bai Wa Taiwan

A yau Laraba, kasar Sin ta bukaci Amurka da ta daina bai wa Taiwan makamai, ta kuma guji yin kafar ungulu ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a mashigin Taiwan.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya bayyana hakan a yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa kullum, lokacin da aka tambaye shi game da rahotannin da ke cewa, gwamnatin Trump ta bayar da dalar Amurka biliyan 5.

3 na taimakon da kasar ke bai wa kasashen waje da aka dakile a kwanan baya, wanda ya hada da dalar Amurka miliyan 870 da aka kebe a kan sha’anin tsaro na Taiwan.

A cewar Lin, Sin ta damu matuka game da ire-iren wadannan rahotanni, yana mai nuni da cewa, a ko da yaushe kasar Sin tana jaddada adawa da taimakon soja da Amurka ke bai wa yankin Taiwan na kasar Sin, saboda irin wannan hali ya saba wa ka’idar “kasar Sin daya tak a duniya” da kuma sanarwar hadin gwiwa guda uku wadanda Amurka da Sin suka fitar, tare da keta ‘yancin kan kasar Sin da muradunta na tsaron kasa, kuma hakan na aikewa da mummunan sako ga dakarun ‘yan aware masu neman wai ‘yancin kan Taiwan. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Iraki Ce Zata Amfana Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka: Inji Sayyed Ammar Hakim

Sayyid Ammar Hakim shugaban jam’iyyar ‘ تيار الحكمة الوطني’ na kasar Iraki ya bayyana cewa kasar Iraki ce kasa ta farko wacce zata amfani da tattaunawa tsakanin Iran da kasar Amurka.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto sayyid hakim yana fadar haka a jiya, ya kuma kara da cewa kasashen Iran da Iraki suna da gangantaka da musulunci makobtaka da kuma al-adu masu yawa. Don haka a duk lokacinda Amurka suka kyautata tsakanin Iran da Amurka kasashen biyu suna iya bude kan iyakokinsu don mu’amala da juna ba tare da Amurka ta shiga tsakanin ba.

A wani waje a cikin jawabinsa Hakim ya amince da ruwan da gwamnatin kasar Amurka ta taka wajen kauda tsohuwar gwamnatin kama karya na sadam Husaini. Da kuma kawo tsarin democradiyya wanda ya bawa mutanen kasar Iraki sararawa daga musibun sadam Husain a kan mutanen kasar.

Ya kuma kammala da cewa ‘amminsa shahid Bakir Hakim’ ya taba fadar cewa akwai bukatar mutanen kasar Iran su tattaunawa tsakaninsu da kasar Amurka don tabbatar da zaman lafiya a yankin Asiya ta kudu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Tace Yarjeniya Da Amurka Mai Yuwa Ne Idan Da Gaske Take
  • Sojojin Kasar Yemen Sun Kai Hare Hare Kan HKI Da Jiragen Yakin Amurka
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Harin Amurka Na Jiya A Yemen Ya Kai 74
  • Amurka Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadancinta Kimani 30 A Duniya
  • Saudiyya da Iran sun jaddada aniyar fadada alakar soji a tsakaninsu
  • Iraki Ce Zata Amfana Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka: Inji Sayyed Ammar Hakim
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasanta
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta
  • Batawa Sin Suna Ba Zai Taimaka Kawar Da Tambarin Amurka A Matsayin Daular Kutsen Intanet Ba
  • Hisbah ta kama matashi yana ‘baɗala’ da Akuya a Kano