Leadership News Hausa:
2025-04-18@22:36:58 GMT

Sin Za Ta Kara Matsa Kaimi Ga Raya Sha’anin Mata Na Duniya

Published: 27th, February 2025 GMT

Sin Za Ta Kara Matsa Kaimi Ga Raya Sha’anin Mata Na Duniya

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian ya bayyana a yau cewa, bana shekara ce ta cika shekaru 30 da gudanar da taron harkokin mata na duniya na Beijing. Kuma kasar Sin za ta ci gaba da amfani da damar da aka samu ta cika shekaru 30 da zartas da sanarwar Beijing da shirin ayyuka, da yin kokari tare da kasahen duniya wajen sa kaimi ga raya sha’anin mata na duniya.

Lin Jian ya bayyana cewa, a ranar 24 ga watan Fabrairu, an gudanar da taron tattaunawa kan murnar cika shekaru 30 da zartas da sanarwar Beijing da shirin ayyuka bisa bukatun Sin da wasu kasashen da abin ya shafa, a yayin da majalisar kare hakkin dan Adam ta MDD ta gudanar da taronta karo na 58, inda shugabannin hukumomin MDD mata suka halarci taron tare da gabatar da jawabi.

Lin Jian ya ce, a matsayin ‘yar sama jannati ta farko ta kasar Sin wadda ta shiga sararin samaniya, Liu Yang ta yi jawabi ta kafar bidiyo cewa, tunanin zaman daidaito na sha’anin binciken sararin samaniya na kasar Sin ya nuna cewa, kasar Sin tana kokarin raya sha’anin mata, wato tabbatar da yanayin yin takara cikin adalci ta bisa kyakkyawan tsari, kuma wannan ne aikin da aka gudanar bisa tunanin sanarwar Beijing. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Nemi Kasashen Duniya Su Taimaka Wa Libya Wajen Fita Daga Kangin Da Take Ciki

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwararru Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Dangane Da Wayewar Kan Sin Da Afirka 
  • Kasar Sin Ta Nemi Kasashen Duniya Su Taimaka Wa Libya Wajen Fita Daga Kangin Da Take Ciki
  • Amurka Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadancinta Kimani 30 A Duniya
  • Matar gwamna ta ɗauki nauyin ragon suna da hidimar duk matar da ta haifi ’yan uku a Sakkwato
  • Matan da suka tsira daga Boko Haram na buƙatar tallafin musamman
  • Sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Kona Yara Da Mata A Harin Da Suka Kai Khum Yunis Na Gaza
  • AGILE: Gwamnatin Kaduna da Bankin Duniya Na Sauya Rayuwar ’Ya’ya Mata Ta Hanyar Ilimi
  • Kasar Pakistan Ta Kara Jaddada Dokar Rashin Amincewa Da HKI A Matsayi Kasa
  • An Yi Kira Ga Jihohi Da Su Kara Samar Da Ingantacciyar Hanyar Kiyon Lafiya
  • An Gudanar Da Taron Kasa da Kasa Don Tallafawa Yan Gudun Hijirar A Sudan