Hukumar fansho ta jihar Jigawa da kananan hukumomin jihar ta fara biyan sama da naira miliyan 733 ga  ma’aikata sama da 280 da suka yi ritaya da kuma ‘yan uwan ​​ma’aikatan da suka rasu.

Shugaban hukumar Dakta Bilyaminu Shitu Aminu ne ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi ga wadanda abin ya shafa a ofishin fansho da ke Dutse babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa kudaden sun hada da na barin aiki,  da na ma’aikatan da suka mutu.

A cewarsa, ma’aikatan 281 sun hada da na jiha, da kananan hukumomi da na hukumar ilimi, wadanda suka yi ritaya na son rai ko kuma sun kai shekarun ritaya ko kuma wadanda suka mutu suna aiki.

Dakta Bilyaminu Shitu ya ci gaba da bayanin cewa  za a biya ma’aikata 208 da suka yi ritaya daga aiki sama da naira 542, yayin da za a biya sama da Naira miliyan 144 ga ‘yan uwan ​​wadanda suka mutu a bakin aiki su 47.

A cewarsa, rukunin karshe su ne ma’aikata 26 da suka yi ritaya daga aiki kuma suka fara karbar fansho duk wata amma sun mutu kafin su kai wa’adin mafi karancin shekaru biyar bayan sun yi ritaya.

Shugaban hukumar ya bayyana cewa jihar Jigawa  na daya daga cikin jihohin da ke da kyakkyawan tsarin fensho mafi inganci a kasar nan, duba da yadda ta ke kokarin biyan wadanda suka yi ritaya ba tare da wata matsala ba kuma akan lokaci.

Ya ce wannan gagarumin ci gaba ya nuna irin yadda gwamnatin jihar ta himmatu wajen kyautata rayuwar ‘yan fanshonta da kuma muhimmancin tabbatar da biyan hakkokin wadanda suka yi wa jihar hidima.

Shugaban ‘yan fanshon ya ce, hukumar ta jajirce wajen tabbatar da biyan kudaden fansho cikin lokaci da inganci kuma tana sa ran za ta ci gaba da yin sabbin abubuwa da nufin inganta jin dadin ‘yan fanshonta.

Biyan kudaden da aka gudanar a hedikwatar hukumar fansho ta jihar Jigawa dake Dutse, wani bangare ne na kokarin karrama kwazon ma’aikatan gwamnati da suka sadaukar da kai wajen yi wa jihar hidima.

Shugaban hukumar ya kuma yabawa Gwamna Malam Umar Namadi bisa irin goyon bayan da yake bai wa hukumar.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, wadanda aka biya hakkokin nasu, sun nuna jin dadinsu da yadda aka biya su akan lokaci.

Sun yi nuni da cewa, biyansu kudaden  zai ba su damar sauke nauyin da ya rataya a wuyansu da kuma inganta rayuwarsu a lokacin ritaya.

 

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa da suka yi ritaya wadanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanin Saudiyya ya haɗa kai da gwamnatin Jigawa kan noman dabino

Samar da dabino zai samu sauyi mai mahimmanci a Jihar Jigawa bayan da wani kamfani daga kasar Saudiyya mai samar da dabino da gwamnatin jihar suka ƙulla yarjejeniya domin ƙara yawan amfanin gona.

Ta wannan haɗin gwiwa za a kawo sababbin fasahohin zamani da irin dabino masu yawa don shigar da su cikin tsarin noma.

Sanata Natasha na neman diyyar N100bn wurin Akpabio Ƙungiya ta rage farashin kayan marmari saboda Azumin Ramadan

A cewar bayanai daga Hukumar Abinci da Aikin Noma ta Majalisar Ɗinkin Duniya (FAO), Saudiyya ita ce ƙasa ta biyu mafi girma wajen samar da dabino na duniya, inda take samar da tan miliyan 1.61 na dabino.

Masar ita ce ƙasa mafi girma wajen samar da dabino, inda ta noma tan miliyan 1.73 na dabino a shekarar 2022, yayin da Aljeriya ke matsayi na uku da tan miliyan 1.25.

Haɗin gwiwar Gwamnatin Jihar Jigawa da wannan rukunin daga Saudiyya tare da Netay Agro-Tech, wani kamfanin amfani da ke Nijeriya ma gudanar da harkokin noma, zai kawo karuwar samuwar dabino a jihar.

Kasar Nijeriya na samar da kusan tan 21,000 na dabino a kowace shekara, inda Jihar Jigawa ke cikin jihohi mafi girma wajen samar da dabino.

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, yayin da yake jawabi lokacin da ya karɓi wata tawaga daga babban kamfanin noma na Saudiyya, wanda ya ƙware wajen shuka dabino da sarrafa gonaki a ofishinsa da ke Dutse, ya ce wannan haɗin gwiwa zai kawo sabon salo ga samar da dabino a Jigawa.

Gwamnan ya bayyana goyon bayan gwamnatinsa ga wannan yunƙuri, yana mai cewa ya dace da ajandar bunkasa aikin gona ta jihar.

“Mun yi maraba da zuwanku Jihar Jigawa tare da nuna godiya ga sha’awar da kuka nuna wajen yin aiki tare da mu.

“A matsayinmu na gwamnati, mun jajirce kan wannan haɗin gwiwa saboda zai amfani al’ummarmu sosai.

“Zuwanku da sha’awar yin haɗin gwiwa da mu wajen kafa gonakin dabino a fadin jihar, da kuma inganta samar da alkama, sun yi daidai da burinmu na bunkasa aikin noma,” in ji gwamnan.

Ya sake jaddada shirinsa na samar da dukkan kayan aiki da ake bukata don tabbatar da nasarar aiwatar da wannan shiri.

Ya bayyana kwarin gwiwa cewa, haɗin gwiwar zai samar da fa’idodi masu ban mamaki tare da mayar da Jigawa ta zama jagora a masana’antar dabino ta duniya.

Shugaban tawagar, Abdul’aziz Abdurrahman-Al-Awf ya jaddada ƙudurinsu na kawo fasahohin noma na zamani zuwa Jihar Jigawa.

“Muna son tabbatar da samar da dabino a duk shekara, ba wai kawai a wasu yanayi ba, kuma haɗin gwiwarmu zai haɗa da horar da manoma da ba wa matasa dama,” in ji shi.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Biya Diyar Sama Da N1.5 Biliyan Ga Wadanda Aikin Tituna Ya Shafa
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Biya Diyar Sama Da Naira Biliyan 5 Ga Wadanda Aikin Tituna Ya Shafa
  • Kamfanin Saudiyya ya haɗa kai da gwamnatin Jigawa kan noman dabino
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kano Ta Tsawaita Wa’adin Biyan Kudin Aikin Hajji
  • Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Nemi Hadin Kan Al’ummar Jihar Jigawa
  • Hukumar JSPCACC Ta Kwato Kudaden Gwamnati Sama Da Naira Miliyan 300
  • Gwamna Namadi Ya Bukaci Wadanda Suka Amfana Da Tallafin Mazabu Su Zama Masu Dogaro Da Kai
  • Hukumar Tsaro Ta Farin Kaya Ta Kama Wasu Mutane 2 Da Yin Sojan Gona
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Aikin Gyaran Titin Birnin Kudu Akan Kudi Naira Biliyan 11.5