Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce Gwamna Umar Namadi ya amince da nadin sabbin jami’an cibiyoyi 27 da za su gudanar da aikin Hajjin shekarar 2025.

Babban Daraktan Hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse babban birnin jihar.

Ya ce, an zabo sabbin jami’an cibiyar ne daga dukkan kananan hukumomin jihar 27, kuma za su samu horo da jagoranci kan ayyukan da hukumar ta dora musu.

Ya kuma bayyana cewa, tuni hukumar ta gudanar ta taron bita ga dukkan jami’an shiyyar da nufin sanar da jami’an irin ci gaban da aka samu a shirye-shiryen gudanar da aikin hajji mai zuwa.

Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya bayyana jin dadinsa kan yadda ake ci gaba da gudanar da harkokin ilimantar da Alhazan game da aikin hajjin.

Ya yi bayanin cewa, an tanadar da  zababbun malaman addinin Islama domin gudanar da aikin bita ga Alhazai da ke gudana a babban masallacin Dutse.

Ya  ce, hukumar jin dadin Alhazai ta jihar ta bullo da sabbin dabaru na ilmantar da Alhazan na bana.

Ya shawarci maniyyata musamman wadanda wannan ne Hajjinsu na farko, da su yi amfani da wannan dama wajen inganta iliminsu na  addini da sauran muhimman bayanai da za su taimaka musu wajen gudanar da aikin hajji karbabbe.

Shugaban ya ce, nan ba da jimawa ba za a rufe  gudanar da taro bitar  har sai bayan watan Ramadan.

Ya ce, taron bitar da hukumar ta gudanar, ya bai wa maniyyatan jihar damar samun ilimin aikin hajji da kuma sanin tsare-tsaren da hukumomin Saudiyya da hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON suka tanadar a aikin hajjin bana.

Don haka, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya yaba wa mahalarta taron bitar, inda ya kara da cewa hakan karin ilimi ne da zai amfane su baki daya.

Da yake tsokaci game da rajistar da ake ci gaba da yi a jihar, shugaban hukumar ya yi kira ga maniyyatan da suka fito daga dukkan kananan hukumomi ashirin da bakwai na jihar da har yanzu ba su kammala biyan kudin ba, su yi kokarin cikawa domin hukumar  NAHCON ta kara wa’adin biyan kudin zuwa mako mai zuwa.

Labbo, ya ce ranar wa’adin zai cika ne a ranar 7 ga watan Maris 2025, inda ya kara da cewa, hukumar ta biya kusan Naira biliyan 6 ga NAHCON.

Ya kuma yabawa jami’an shiyyar da suka yi rijista, tare da tattara kudaden ajiyar hajji a yankunansu.

Shugaban hukumar, ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa amincewa da sabbin jami’an cibiyar da kuma goyon baya da hadin kai da ake ba hukumar a kowane lokaci.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa gudanar da aikin

এছাড়াও পড়ুন:

Cibiyar Nazarin Jinsi (CGS) Da Jami’ar Bayero Kano Za Su Yi Aiki Tare

Cibiyar Nazarin Jinsi (CGS) Jami’ar Bayero Kano BUK ta jaddada aniyar ta na ci gaba da ayyukan da suka shafi jinsi ta hanyar sabunta aikinta da kuma inganta karfinta na ma’aikata.

 

 

Darakta CGS, Dakta Ambasada Safiya Nuhu, ta bayyana haka a lokacin da ta kai ziyarar ban girma ga Shugaban jami’ar Farfesa Sagir Adamu Abbas.

 

 

Ta ba da tabbacin mataimakiyar shugabar gudanarwa ta CG ta ci gaba da ba da goyon baya wajen tinkarar al’amuran al’umma, musamman wajen karfafa dabi’un iyali, inganta al’adun gargajiya, da kuma haifar da kyakkyawar tarbiyya.

 

 

Dokta Safiya ta jaddada cewa sabbin nade-naden mukaman da aka yi wa mataimakan daraktoci na cibiyar na nuni da yadda jami’ar ta yi hadin gwiwa wajen tunkarar kalubalen da ke addabar al’umma ta hanyar binciken da ya shafi jinsi da hada kan al’umma.

 

 

Ta bayyana cewa Cibiyar za ta yi bikin cika shekaru 10 a shekarar 2025 kuma ta kara himma a shirye-shiryen horarwa, bincike, hadin gwiwa, da ayyuka masu tasiri.

 

 

“Wani sanannen haɗin gwiwa shine shirin “Ilimi don Canji”, ƙoƙari na haɗin gwiwa tare da jami’o’i a Kanada da Uganda da nufin magance matsalolin da suka danganci jinsi ta hanyar bincike da haɓaka iyawa”

 

 

A nasa jawabin, Shugaban jami’ar Farfesa Sagir Adamu Abbas ya yabawa cibiyar kan sababbin ayyukanta.

 

 

Farfesa Sagir ya kwadaitar da cibiyar da ta binciko sabbin hanyoyin magance kalubalen da mata da matasa ke fuskanta a wannan zamani da suka hada da shaye-shayen miyagun kwayoyi, da kuma yin amfani da kwarewarta wajen samun kudade na ciki da waje domin dorewa.

 

Rel/Khadijah Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Maniyatan Bana A Jigawa
  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa
  • Hukumar Alhazai ta Jigawa Ta Shirya Bitar Ga Malaman Bita na Kananan Hukumomi 27
  • Cibiyar Nazarin Jinsi (CGS) Da Jami’ar Bayero Kano Za Su Yi Aiki Tare
  • KADGIS Za Ta Yi Amfani Da Sabuwar Manhajar Biyan Diyyar Filaye A Kaduna
  • KADGIS Ta Samar Da Sabuwar Manhajar Biyan Diyyar Filaye A Kaduna
  • Jigawa Za Ta Zama Cibiyar Binciken Lafiya Nan Ba Da Jimawa Ba – Gwamna Namadi
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Neja Ta Fara Rabon Unifom da Jakunkunan Hannu Ga Maniyya
  • Minista Ya Gargaɗi Jami’an Gwamnati Kan Rashin Sanin Ilimin Tantance Ingantattun Labarai
  • Hajj 2025: Hukumar Alhazai Ta Shirya Taron Bita Ga Mahajjata a Jihar Kwara