HausaTv:
2025-02-27@08:42:46 GMT

Iran Da Saudiyya Sun Tattauna Kan Taron OIC Mai Zuwa

Published: 27th, February 2025 GMT

Kasashen Iran da kuma Saudiyya sun tattauna kan halin da ake ciki a yankin dama batun taron kungiyar kasashen Musulmi ta OIC da za’ayi a cikin kwanaki masu zuwa a Jeddah.

Tattaunawar ta wakana ne ta wayar tarho tsakanin ministan harkokin wajen Saudiyya Yarima Faisal bin Farhan da Abass Araghchi, ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran (RII).

A yayin ganawar, bangarorin biyu sun yi nazari kan halin da ake ciki a yankin, tare da tattauna taron ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar OIC da za a yi a Jeddah.

Dama a kwanan baya bangarorin sun tattauna kan shirin shugaban Amurka Donald Trump na kwace zirin Gaza dama tilasta wa falasdinawan yankin kaura zuwa Masar da Jordan, shirin da dukkan kasashen biyu sukayi fatali da shi.

Araghchi ya la’anci shirin na Amurka da ‘yan sahyoniya na tilastawa al’ummar Gaza komawa wasu kasashe a matsayin ci gaba da shirin ‘yan mulkin mallaka na shafe Falasdinu, yana mai jaddada bukatar daukar kwararan matakai na kasashen duniya don tunkarar wannan makirci.

Ya kuma yi kira ga al’ummar musulmi da sauran al’ummar duniya baki daya da su dauki matakin gaggawa kan lamarin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Zimbabwe Ya Kaddamar Da Yankin Masana’antu Da Sin Ta Zuba Jari

Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa a ranar Litinin ya halarci bikin kaddamar da gina yankin masana’antu da kasar Sin ta zuba jari, inda ya bayyana shi a matsayin wani ci gaba na bunkasa masana’antu a kudancin Afirka.

Kamfanin Xintai Resources na kasar Sin ne ya zuba jarin dala biliyan 3.6 a yankin masana’antu musamman na makamashi da karafa na kogin Palm da ke Beitbridge na lardin Matabeleland ta kudu, kuma za a aiwatar aikin a matakai biyar cikin shekaru 12, da nufin samar da kayayyakin da ake amfani da su na chromium da coke.

Mnangagwa ya ce, “Ina fatan aikin wannan yankin masana’antu na musamman, zai taka rawa a matsayin wani muhimmin tubali ga ci gaban masana’antu da zamanantar da al’ummarmu. Muna sa ran wannan aikin zai taimaka wajen ciyar da tattalin arzikin kasarmu gaba da kuma bude hanyoyin da ba a taba ganin irinsu ba wajen samar da ayyukan yi, da ci gaban fasaha, da ci gaban zamantakewa,”

Ya ce, aikin wani babban ci gaba ne ga hanyar da Zimbabwe ke bi wajen bunkasa masana’antu saboda ya hada aikin samar da makamashi da karafa, bangarori biyu masu muhimmanci da ke da damar sake fayyace yanayin masana’antu na kasar. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sheikh Na’im Kasim Ya Gana Da Ministan Harkokin wajen Kasar Iran Da Shugaban Majalisar Dokoki
  • Gwamnatin Katsina Ta Ƙaddamar Da Shirin Tallafin Abinci Na Naira Biliyan 4
  • Kamfanin Saudiyya ya haɗa kai da gwamnatin Jigawa kan noman dabino
  • Shugaban Zimbabwe Ya Kaddamar Da Yankin Masana’antu Da Sin Ta Zuba Jari
  • Ministan Harkokin Wajen Rasha Ya Fara Ziyarar Aiki A Nan Tehran
  • Iran : Makaman Kare Dangi Na Israila Barazana Ne Ga Zaman Lafiya Da Tsaro
  • Kasashen Kawancen Sahel Sun Kadaddamar Da Tutar Kungiyar
  • Xi Ya Tattauna Da Putin Ta Wayar Tarho 
  • Kasashen Sin da Afirka ta Kudu sun kara zurfafa alakar da ke tsakanin juna