HausaTv:
2025-04-18@22:42:03 GMT

Masar Ta Yi Watsi Da Shawarar Cewa Ta Karbi Ragamar Gaza Na Wucin Gadi

Published: 27th, February 2025 GMT

Masar ta yi watsi da shawarar da jagoran ‘yan adawar Isra’ila Yair Lapid ya gabatar na cewa Alkahira, maimakon kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas, ta karbi ragamar zirin Gaza na wucin gadi, tana mai danganta irin wadannan tsare-tsare da cewa “ba za a amince da su ba.”

Kamfanin dillancin labarai na MENA ya nakalto kakakin ma’aikatar harkokin wajen Masar Tamim Khalaf yana cewa, “Duk wani ra’ayi ko shawarwari da suka saba wa matsayar Masar da Larabawa (a kan Gaza) an yi watsi da su kuma ba za a amince da su ba.

Kakakin ya nanata kiran da Masar ta yi na janyewar Isra’ila daga yankunan Falasdinawa da ta mamaye, da kuma goyon bayanta ga kafa kasar Falasdinu mai cin gashin kanta.

Mista Khalaf ya jaddada “dangantaka ta zahiri” tsakanin Gaza, yammacin gabar kogin Jordan da ta mamaye da kuma gabashin al-Quds, yana mai cewa suna wakiltar “yankin kasar Falasdinu mai cin gashin kanta kuma dole ne su kasance karkashin cikakken ikon mallakar Falasdinawa da gudanar da mulki.”

A ranar Talata ne, Yair Lapid na Isra’ila ya gabatar da wani shiri na Gaza bayan kawo karshen yakin.

A karkashin shirin nasa, Masar za ta karbi ragamar tafiyar da yankin da zarar an kammala yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

“Mafita ita ce Masar za ta dauki nauyin gudanar da Zirin Gaza na tsawon shekaru takwas tare da zabin tsawaita shi zuwa shekaru 15,” kamar yadda ya shaida wa kungiyar Haukish Foundation for Defence of Democracy (FDD) a Washington.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Minista Ya Zargi Isra’ila Da Kasashen Yammacin Turai Da Kitsa Kashe-kashen Rayuka A Nijeriya 

Tsohon ministan sufurin jiragen sama, Femi Fani-Kayode, ya yi kakkausar suka dangane da yawaitar kashe-kashen da ake yi a jihar Filato da sauran sassan Arewacin Nijeriya, inda ya dora laifin kitsa tashe-tashen hankula da nufin tada zaune tsaye a Nijeriya. A wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta, Fani-Kayode ya yi ikirarin cewa wadanda ke haddasa tashe-tashen hankula ba wai kawai ’yan tada kayar baya ba ne, a’a, wasu ‘yan kasashen waje ne da ake zargin suna shigowa Nijeriya ta kan iyakokin kasar, da nufin raba kan al’ummar kasar ta hanyar addini da kabilanci. Hadin Gwiwar Kasashen Asiya Da Afirka Na Habaka Karfinsu Na Dogaro Da Kai Da Cin Moriya Tare Yaukaka Zumunci Da Makwabta A Aikace Tsakanin Sin Da Malaysiya “Suna shigowa su yanka mutanenmu, suna kashe Kirista da Musulmi, ’yan Arewa da ’yan Kudu,” inji shi. “Suna so su hargitsa kasar nan, kuma su bata sunan gwamnati, an taba kitsa irin hakan kuma har yanzu ana sake kitsa hakan.” Da yake zayyana makamancin haka, Fani-Kayode ya yi gargadin cewa, rikicin da ake fama da shi na da kamanceceniya da yadda aka kirkiri tashe-tashen hankula a zabukan shekarar 2015, inda tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya fuskanci irin wannan tashin hankali. “Haka aka shirya a shekarar 2014 kafin a kayar da Goodluck Jonathan, yanzu kuma sun fara shirin irin haka domin tunkarar 2027,” in ji shi. “Mun san su wane ne, kasashen waje daga cikin kasashen Yamma da Isra’ila da wasu da dama. Ba sa son kwanciyar hankali a Nijeriya.” Fani-Kayode ya yi kira ga gwamnatocin jihohi da na tarayya da su kara daukar kwararan matakai. Ya bukaci gwamnatin jihar Filato da ta kara kaimi sosai sannan ya bukaci da a kara sa ido kan iyakokin Nijeriya. Ya karkare da sakon hadin kai da juriya da kishin kasa, “Nijeriya za ta ci gaba da wanzuwa, Nijeriya ba za ta fadi ba, za mu taka matsayi kan matsayi, kuma dimokuradiyyarmu za ta dore da nufin Allah, kuma mu tsaya a dunkule wuri daya. Allah ya tsare Nijeriya.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Ta Sake Aiwatar Da Kisan Kiyashi A Sansanin Falasdinawa Na Jabaliya
  • Hamas ta gabatar da shawara kan yarjejeniyar musayar fursunoni da tsagaita wuta
  • Wata Cibiyar Kare Hakkin Bil’Adama Ta Bukaci Kama Jami’in Haramtacciyar Kasar Isra’ila A Kasar Birtaniya
  • Sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Kona Yara Da Mata A Harin Da Suka Kai Khum Yunis Na Gaza
  • Tsohon Minista Ya Zargi Isra’ila Da Kasashen Yammacin Turai Da Kitsa Kashe-kashen Rayuka A Nijeriya 
  • Kasar Pakistan Ta Kara Jaddada Dokar Rashin Amincewa Da HKI A Matsayi Kasa
  • Hamas ta bukaci hadin kan duniya domin kawo karshen kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a Gaza
  • A Kalla Mutane 9 Ne Su Ka Yi Shahada A Gaza
  • Amurka Tana Shirin Mikawa HKI Dubban Boma-Bomai Cikin Makonni Masu Zuwa
  • Hamas Ta Fadawa Iyalan Yahudawan Da Take Tsare Dasu A Gaza Kan Cewa ‘Ya’yansu Zasu Koma A Cikin Akwatunan Gawaki