HausaTv:
2025-03-29@21:11:33 GMT

Masar Ta Yi Watsi Da Shawarar Cewa Ta Karbi Ragamar Gaza Na Wucin Gadi

Published: 27th, February 2025 GMT

Masar ta yi watsi da shawarar da jagoran ‘yan adawar Isra’ila Yair Lapid ya gabatar na cewa Alkahira, maimakon kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas, ta karbi ragamar zirin Gaza na wucin gadi, tana mai danganta irin wadannan tsare-tsare da cewa “ba za a amince da su ba.”

Kamfanin dillancin labarai na MENA ya nakalto kakakin ma’aikatar harkokin wajen Masar Tamim Khalaf yana cewa, “Duk wani ra’ayi ko shawarwari da suka saba wa matsayar Masar da Larabawa (a kan Gaza) an yi watsi da su kuma ba za a amince da su ba.

Kakakin ya nanata kiran da Masar ta yi na janyewar Isra’ila daga yankunan Falasdinawa da ta mamaye, da kuma goyon bayanta ga kafa kasar Falasdinu mai cin gashin kanta.

Mista Khalaf ya jaddada “dangantaka ta zahiri” tsakanin Gaza, yammacin gabar kogin Jordan da ta mamaye da kuma gabashin al-Quds, yana mai cewa suna wakiltar “yankin kasar Falasdinu mai cin gashin kanta kuma dole ne su kasance karkashin cikakken ikon mallakar Falasdinawa da gudanar da mulki.”

A ranar Talata ne, Yair Lapid na Isra’ila ya gabatar da wani shiri na Gaza bayan kawo karshen yakin.

A karkashin shirin nasa, Masar za ta karbi ragamar tafiyar da yankin da zarar an kammala yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

“Mafita ita ce Masar za ta dauki nauyin gudanar da Zirin Gaza na tsawon shekaru takwas tare da zabin tsawaita shi zuwa shekaru 15,” kamar yadda ya shaida wa kungiyar Haukish Foundation for Defence of Democracy (FDD) a Washington.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Maduro Ya Bayyana Sakataren Harkokin Wajen Amurka Da Cewa Wawa Ne

Shugaban kasar Venezuela Nicolas Maduro ya bayyana sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio da yake ziyarar aiki a kasar Guyana da cewa, sakarai ne.

A yayin ziyarar da sakataren na  harkokin wajen Amurka ya kai zuwa kasar Guyana mai makwabtaka da Venezuela, ya ce, Amurka za ta mayar da martani mai karfi akan Venezuela idan har ta kai wa Guyanan hari.

Rubio ya kara da cewa; Idan haka ta faru, to kuwa Venezuela za ta gwammace kida da karatu a wannan rana.

Amurkan dai ta kulla yarjejeniyar tsaro da kasar ta Guyana a yayin ziyarar da Rubio ya kai.

Shi kuwa shugaban kasar ta Venezuela da yake mayar da martani ya ce; Marco Rubio wawa, ya zo yana yi wa kasar Venezuela barazana daga kasar Guyana, sannan ya kara da cewa; Venezuela ta fi karfin a yi mata barazana, domin ita kasa ce ta ‘yanci.”

Alaka a tsakanin Venezuela ta Amurka ta sake tabarbarewa tun bayan da shugaba Donald Trump ya hau karagar mulki, bayan da ya kara kakaba mata takunkumai, da kuma batun mayar da ‘yan hijirar kasar daga Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas ta yi Tir da kakkausar murya da harin Isra’ila kan masu aikin ceto a Gaza
  • Wani Jami’in Leken Asirin HKI Ya Bukaci Kasashen Afirka Su Taimaka Su Karmi Falasdinawan Da Za;a Kora Daga Gaza
  • Kwamandan IRGC Ya Gargadi Amurka Dangane Da Hari Kan Kasar A Ranar Qudus Ta Duniya
  • Maduro Ya Bayyana Sakataren Harkokin Wajen Amurka Da Cewa Wawa Ne
  •  Sojojin Iran: Gwagwarmaya Ce Kadai Hanyar Warware Matsalar Falasdinu
  • Wakilin Sin: Dole Ne A Mutunta Hakki Mai Tushe Na Palasdinawa
  • Iran, Lebanon, Iraki, Yemen sun fara atisayen hadin gwiwa na goyan bayan Gaza
  • MDD ta yi gargadi game da tabarbarewar al’amuran jin kai a Gaza
  • Isra’ila ta sake kashe wani kakakin Hamas
  • Isra’ila : An yi zanga zangar adawa da gwamnatin Netanyahu a Tel-Aviv