HausaTv:
2025-03-29@21:13:50 GMT

Isra’ila Ta Saki Fursunonin Falasdinawa Da Dama

Published: 27th, February 2025 GMT

Isra’ila ta saki fursunonin Falasdinawa da dama a daidai lokacin da kungiyar Hamas ta mika gawarwakin ‘yan Isra’ila hudu ga kungiyar agaji ta Red Cross.

Fursunonin sun isa birnin Ramallah da ke gabar yammacin kogin Jordan ne a kan motocin kungiyar agaji ta Red Cross bayan sun tashi daga gidan yarin Ofer da ke yankin da aka mamaye.

Musayar ta karkare kashi na farko na musayar da aka faro tsakanin bangarorin biyu, wanda ke gudana a karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka fara aiwatarwa a watan da ya gabata da fatan kawo karshen yakin kisan kare dangi da gwamnatin Isra’ila ta yi wa Gaza na tsawon watanni 15.

Falasdinawan da aka sako na cikin fursunoni sama da 600, wadanda gwamnatin kasar ta ce za ta saki a matakin farko.

Baki daya, a matakin farko kungiyar Hamas ta mika ‘yan Isra’ila 33 da ta yi garkuwa dasu da suka hada da gawarwaki takwas, domin musayar fursunonin Falasdinawa kusan 2,000.

Tun ranar Asabar data gabata ce ya kamata gwamnatin Isra’ila ta mika fusunonin Falasdinawan su 206, saidai Isra’ila ta jinkirta sakin fursunonin bayan da kungiyar Hamas ta mika wasu ‘yan Isra’ila shida daga Gaza, tana mai cewa Hamas na wulakanta ‘yan kasarta a yayin bikin mika su.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Miliyoyin mutane sun gudanar da jerin gwanon ranar Qudus

Miliyoyin al’umma daga sassa daban daban na duniya sun gudanar da jerin gwanon zagayowar ranar Kuds ta duniya wacce ta gudana yau.

An dai kebance ranar ce domin nuna goyan baya ga al’ummar falasdinu, kuma ana gudanar da ita ne a ko wacce Juma’ar karshe ta watan ramadana bisa fatawar jagoran juyin juya halin musulinci na Iran Ayatollah Khumeiny.

A Iran ma kamar sauren sassan duniya jama’a sun fito kan tituna domin gudanar da bukukuwan ranar Qudus ta duniya, inda suke bayyana goyon bayansu ga Falasdinawa tare da yin tir da kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a zirin Gaza.

An kuma yi irin wannan gangamin a kasashe da dama na yankin yammacin Asiya da suka hada da Iraki da Yemen da Lebanon da kuma wasu da dama a fadin duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas ta yi Tir da kakkausar murya da harin Isra’ila kan masu aikin ceto a Gaza
  • Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)
  • Kungiyar “White Helmets Ta” A Kasar Siriya Ta Rasha Tallafin Da Take Samu Daga USAID
  • Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki
  • Gwamnatin Kaduna Ta Jadadda Kudurin Ta Wajen Samarda Tsaftatacen Ruwan Sha Ga Al’umma 
  • Miliyoyin mutane sun gudanar da jerin gwanon ranar Qudus
  • GORON JUMA’A 28-03-2025
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Hana Baƙin Haure Shigowa Nijeriya Ba Bisa Ƙa’ida Ba
  • Isra’ila ta sake kashe wani kakakin Hamas
  • Isra’ila : An yi zanga zangar adawa da gwamnatin Netanyahu a Tel-Aviv