NAJERIYA A YAU: Halin da jama’a za su shiga idan Kamfanin Kaduna Electric ya ƙi sauraren ma’aikatansa?
Published: 27th, February 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Wutar lantarki a Najeriya ta zama ginshiƙin rayuwa da al’umma ba sa iya rayuwa ba tare da ita ba. A duk lokacin da aka ɗauke ta al’umma kan shiga matsanancin hali.
Mutane da dama sun dogara ne da wutar lantarki wajen tafiyar da harkokinsu na yau da kullum, kai har ma da na kasuwanci.
A kwanakin baya ne jihohin Kaduna, Sakkwato, Zamfara da kuma Kebbi suka fuskanci ɗaukewar wutar lantarki na tsawon kwanaki, wanda ya jefa al’ummar jihohi cikin halin ni-’yasu.
NAJERIYA A YAU: Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi? DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son HaihuwaShirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan halin da al’ummar jihohin da ke ƙarƙashin kulawar kamfanin rarraba wuta na Kaduna Electric za su shiga idan ma’aikatan kamfanin suka shiga yajin aiki.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Lantarki Wutar Lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Dan kwallon Najeriya ya mutu bayan fadowa daga bene a Uganda
Wani dan kwallon Najeriya mai suna Abubakar Lawal daga Jihar Sakkwato ya rasu bayan fadowa daga bane a kasar Uganda, inda yake taka leda.
Rahotanni sun bayyana cewa Abubakar Lawal mai shekaru 29 ya gamu da ajalinsa ne bayan ya fado daga hawa na uku na wanin babban kantin sayar da kayayyaki a Kampala, babban birnin kasar Uganda.
Rasuwar tasa ta haifar haifar da ce-ce-ku-ce a kasar, kamar yadda kafofin yada labarai suka ruwaito. Da farko an alakanta rasuwar tasa da hatsarin babur, kafin daga bisani jami’an tsaro su bayyana cewa ya fado ne daga bene.
Marigayin dan wasan gaba ne a kungiyar kwallon kafa ta Vipers da ke kasar, inda ya fara wasa tun shekara 2022, kafin nan ya shekara biyu yana taka lelda a kungiyar AS Kigali da ke kasar Rwanda.
Kungiyar Vipers ta sanar Abubakar ya rasu ne a ranar Litinin bayan da ya fado daga hawa na uku da kataferen kantin mai suna Voicemall Shopping Arcade a Kampala.
A sakon ta’aziyyarta, kungiyar ta bayyaan marigayin a matsayin, “mutumin kirki mai kyakkyawar zuciya, mai yawan kyauta ne da kuma taimaka wa jama’a,” kamar yadda ya wallafa a shafinta na X.
Runudar ’yan sandan ta sanar da fara bincike kan musabbabin mutuwar dan kwallon na Najeriya.
Hukumar ’yan sandan Uganda ta bayyana cewa dan wasan ya gamu da ajalinsa ne a lokain da ya kai wa wata kawarsa ’yar kasar Tanzaniya ziyara a rukunin ginin.
A sakon ta’aziyyar dan wasan, kungiyar Nasarawa United, tsohuwar kungiyar Abubakar, ta ce, “Muna jimaminin mutuwar fuju’ar tsohon dan wasanmu Abubakar Lawal, kuma muna rokon Allah Ya sada shi da rahama.”
Shi kuwa Mustafa Kizza, dan wasan Uganda, ya ce: “Rashin Lawal abu ne mai wuyar jurewa. Mutumin kirki ne mai fara da hazaka da ba za mu taba mantawa da shi ba.”