Gwamnatin Jihar Nasarawa ya hori Kiristoci masu niyyar ziyarar su zama jakadu na gari tare dayin addu’ar zaman lafiya, hadin kai, da ci gaba idan sun isa can.

 

Gwamna Abdullahi Sule ya bayyana haka a lokacin bankwana da masu ziyarar su 162 da zasu tashi zuwa Isra’ila.

 

Gwamnan ya jaddada muhimmancin da’a a yayin tafiyar tasu, inda ya bayyana cewa su dauka su Allah ya nufa da wannan ziyarar a bana.

 

Ya kuma tabbatar wa maziyartan jihar cewa gwamnatin jihar ta himmatu wajen kyautata rayuwarsu, tare da samar da matsuguni da abinci kyauta a tsawon tafiyarsu.

 

Sakataren zartarwa na hukumar jin dadin hukumar kula da masu ziyarar kiristoci ta jihar Nasarawa, Davide Ayiwa, wanda ya yabawa gwamnatin jihar kan gyaran ofishin hukumar ya kuma bukaci maziyartan da su ci gaba da gudanar da aikinsu.

 

Bikin ya samu halartar mataimakin gwamnan jihar Dr. Emmanuel Akabe da alkalin alkalan jihar, Mai shari’a Aisha Bashir Aliyu, kwamishiniyar yada labarai da sauran kwamishinoni da sakataren gwamnatin jihar Labaran Shu’iabu Magaji babban akanta janar na jihar.

 

COV/Aliyu Muraki/Lafia

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: nasarawa Ziyara

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Nemi Hadin Kan Al’ummar Jihar Jigawa

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Jigawa ta bukaci  hadin kan al’ummar jihar domin samun nasarar ayyukan da ta sanya a gaba.

Shugaban Hukumar Korafe-korafen Jama’a da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Jigawa (JSPCACC) Barista Salisu Abdu ya bayyana a matsayin wani muhimmin mataki na ci gaba da kokarin tabbatar da gaskiya da rikon amana a bangaren gwamnati.

Ya furta haka ne a lokacin bude taron wayar da kan jama’a na yini 3 da hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Jigawa ta shirya a cibiyar bunkasa ma’aikata dake Dutse.

Ya jaddada cewa, gaskiya, da  rikon amana, su ne ginshikin gudanar da shugabanci nagari.

Barista Salisu Abdu, ya kuma yi kira da a hada kai tsakanin Hukumar da hukumomin gwamnati domin yakar cin hanci da rashawa yadda ya kamata.

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, taron ya hada manyan masu ruwa da tsaki, da suka hada da wakilai daga ma’aikatar shari’a, shari’a, da ICPC, da EFCC, da PCC, inda aka mayar da hankali wajen ilmantar da mahalarta taron game da aikin hukumar, da tsarin shari’a, da kuma bangarorin hadin gwiwa.

Tattaunawar ta ta’allaka ne kan ingantattun ayyuka, da hanyoyin hana almundahana da ayyukan rashawa.

Taron bitar wanda ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ma’aikatan gwamnati, da masu ruwa da tsaki, ya yi nuni da yadda gwamnati mai ci ke kokarin inganta shugabanci nagari da kawar da cin hanci da rashawa domin share fagen samun ci gaba mai ma’ana a jihar.

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Nada Jami’an Alhazai 27 Tare Da Kara Wa’adin Biyan Kudin Aikin Hajji
  • Hamas ta yi tir da matakin Isra’ila na shirin takura masu ibada a masallacin Quds
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kano Ta Tsawaita Wa’adin Biyan Kudin Aikin Hajji
  • Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Nemi Hadin Kan Al’ummar Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Neja Ta Haramta Karbar Haraji A Hannun Masu Kananan Sana’o’i
  • Ministan Harkokin Wajen Rasha Ya Fara Ziyarar Aiki A Nan Tehran
  • Gwamna Namadi Ya Bukaci Wadanda Suka Amfana Da Tallafin Mazabu Su Zama Masu Dogaro Da Kai
  • Hajj 2025: NAHCON Ta Rage N54bn Daga Kudaden Cajin Maniyyata
  • NAHCON Ta Rage N54bn Daga Kudaden Cajin Maniyyata, Ta Tsawaita Rajistar Hajjin 2025