Gwamnatin Kwara Ta Kaddamar Da Kwas Ga Dalibai Makarantun 50
Published: 27th, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Kwara ta kaddamar da shirin horas da makarantun firamare da kananan makarantun gwamnati 50 a fadin jihar domin su iya amfani da fasahar ziyyana shafin internet.
Da yake gabatar da shirin a madadin Gwamna Abdulrahman AbdulRazaq a Makarantar Sakandare ta Bishop’s Smith Junior Ilorin, babban mai ba gwamna shawara na musamman, Alhaji Sa’adu Salau, ya ce shirin na dijital ya kasance don ƙarfafa fannin ilimi.
A cewarsa shirin ya shafi sama da dalibai 150 a kowace makarantu 50 na gwamnati a matakin gwaji.
Ya ce idan aka kafa harsashin tsarin zamani, yaran jihar Kwara ba za su koma baya a tsakanin takwarorinsu na duniya ba.”
Gwamna AbdulRazaq yace sauran makarantun gwamnati da za su ci gajiyar wannan karimcin a babban birnin kasar sun hada da makarantar Sarauniya Elizabeth, Makarantar Grammar Ilorin, da kuma makarantar firamare ta Sheikh Alimi.
A nasa bangaren, mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Kwara kan harkokin dijital da kirkire-kirkire, Ishola Kayode, ya ce manufar shirin shi ne tabbatar da cewa daliban makarantun gwamnati ba su koma baya ba a duniyar dijital.
Ya ce daliban za su zama masu ilimin zamani, inda ya ce za su iya magance matsalolin da ke addabar al’ummarsu.
Ya ce za a fadada shirin bayan tantance bayanan da aka yi.
A nata jawabin shugabar makarantar Bishop’s Smith College (Junior Session), Mrs Akanbi Janet Ayoola, ta ce aikin na daya daga cikin mafi kyawun shawarar da gwamnatin jihar ta dauka a zamanin da fasahar sadarwa da fasahar kere-kere suka zama abin bukata na rayuwa.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati Ta Ba da Umarnin Tafiya Yi Wa Ƙasa Hidima Ga Duk Masu HND
Yawancin wadanda suke da HNd basu samu damar tafiya aikin Yiwa kasa Hidima/Aikin Bautawa kasa wanda hakan ne kuma aka gay a kamata ayi masu adalci kan lamarin
Sai dai kuma irin ci gaban da aka samu ya kawo ko samar da wata matsala ta yadda wadanda suka yi karatun suka kammala a makaranta sai ta kasance wasu daga cikinsu basu samu damar tafiya aikinyiwa kasa hidima ba saboda irin karatun da suka yi.
Da yake bada ta shi gudunmawa darekatan lamurran ‘yan jaridu da hulda da jama’a ma’aikatar ilimi ta tarayya Boriowo Folasade, ya fitar da sanarwa wadda take tabbatar da gaskiyar lamarin na abubuwan da suka biyo bayan dukkan tarurrrukan da kuma ganawar da aka yi.
Sanarwa ta nuna cewa sabon matakin da aka dauka wani abin farincikine ga wadanda suka kammala karatun da ake samun Babbar difiloma ta kasa HNd wadanda a baya ba a basu damar tafiya wuararen da za su yiwa kasa hidima ba.
An ma bayyana cewar matakan da ma’aikatar ilimi ta tarayya ta dauka na tabbatar da cewar ana yin adalci ya kasance ana tafiya da kowa a lamarin ilimi na Nijeriya.
Su ma wadanda suka kammala karatun nasu ba irin na wadanda suka zauna a makaranta ba, suma za su iya je aikin yiwa kasa hidima na shekara daya da takwarorin su wadanda suka samu ko karatun da ya basu damar samun digiri suke yi.
Domin samu daukar mataki wanda ba’a vata lokaci ba an umarci Hukumar kula da ilimin daya shafi fasaha da kere- kere (NBTE)ta gaggauta samar da bayanai na wadanda suka kammala HNd domin tafiya harkar ta yi wa kasa hidama NYSC.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp