Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta sake jaddada aniyar ta na dakile yaduwar magungunan jabun a fadin kasar nan.

 

Darakta Janar na Hukumar Farfesa Mojisola Christianah Adeyeye ta bayyana hakan a yayin bikin bude taron wayar da kan jama’a na kwanaki biyu da aka gudanar a Kano.

 

Farfesa Mojisola Christianah wacce Darakta Pharmacist, Pharmacist Bitrus Fraden ta wakilta ta ce NAFDAC ta bullo da wasu sabbin tsare-tsare guda uku da nufin inganta hanyoyin magance yaduwar magungunan jabu a kasar.

 

Babban Daraktan ya jaddada bukatar masu ruwa da tsaki su tallafa wa wadannan tsare-tsare, da nufin tabbatar da samar da ingantattun kayayyakin kiwon lafiya, masu inganci ga ‘yan Nijeriya.

 

Ta ce Najeriya ita ce kasa ta farko a Afirka da ta fara amfani da wannan fasahar, wanda ke baiwa masu ruwa da tsaki damar ganowa da kuma watsi da kayayyakin da basu da inganci.

 

“Dokar hukumar kula da lafiyar yara ta NAFDAC mai lamba 2024 wata ka’ida ce ta musamman da ke magance bukatu na musamman na yara. Wannan ka’ida ta ginu ne a kan tsarin rijistar da ake da shi, yana ba da karin kariya don tabbatar da tsaro da ingancin kayayyakin kiwon lafiya ga yara.”

 

A nata bangaren wata mataimakiyar darakta Regina Garba ta ce makasudin taron shi ne wayar da kan masu ruwa da tsaki kan hadin gwiwa ta wannan fanni.

 

 

Ko’odinetan NAFDAC na shiyyar Arewa maso Yamma Mista Fadi Nantim Mullah ya ce makasudin gudanar da taron bitar a shiyyar ya kasance ne saboda yawaitar masu sana’ar magunguna musamman a Kano.

 

Abdullahi Jalaluddeen Kano

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Bukaci Kafa Dokar Hukuncin Kisa Ga Masu Safarar Da Shan Miyagun Kwayoyi

 

An bukaci Majalisar Dokoki ta Kasa da ta kafa doka wacce za ta tanadi hukuncin kisa ga masu safarar da kuma masu shan miyagun kwayoyi, domin kare rayuwar ‘yan kasa.

Wannan kiran ya fito ne daga shirin KAKAKI na FRCN Kaduna FM, inda masu kira suka bayyana ra’ayoyinsu a yayin tattaunawa da mai gabatar da shirin.

Masu magana sun nuna damuwa kan illar safarar miyagun kwayoyi a kasar, musamman yadda yake shafar matasa, wadanda ake kallon su a matsayin shugabannin gobe.

Alhaji Gaddafi Rigasa da Hajiya Aisha Mando sun jaddada bukatar hukumomin tsaro su kara zage damtse wajen yaki da wannan matsala, domin inganta ci gaban tattalin arziki da zamantakewa.

Sai dai sun kuma ba da shawarar a farfado da masana’antu a yankin Arewa a matsayin hanya daya daga cikin hanyoyin rage rashin aikin yi, wanda ke haddasa lalacewar matasa da kuma tabarbarewar tsaro.

SULEIMAN KAURA

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Sule Ya Hori Masu Ziyarar Ibada Ta Kirista Su Zama Jakadu Na Gari
  • Sojojin Iran Sun Kammala Atisayen Zulfikar 1403 Da Faretin Sojojin Ruwa
  • Ƙungiya ta raba wa marayu da mabuƙata kayan makaranta a Kano
  • Ƙungiya ta raba wa marayu da mabuƙa kayan makaranta a Kano
  • Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Nemi Hadin Kan Al’ummar Jihar Jigawa
  • EFCC Ta Gurfanar Da Wasu ‘Yan China 16 Da Ake Zargi Da Aikata Zamba Ta Yanar Gizo A Legas
  • An Bukaci Kafa Dokar Hukuncin Kisa Ga Masu Safarar Da Shan Miyagun Kwayoyi
  • Amurka Ta Laftawa Iran Wasu Sabbin Takunkumai
  • NAJERIYA A YAU: Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi?