Shugaban Hafsan Sojan Sama, Air Marshal Hasan Abubakar ya zama Shugaban Kungiyar Sojojin Sama na Afrika-AAAF.

 

Da yake jawabi a wajen taron shugabannin sojojin saman Afrika da aka gudanar a kasar Zambiya, Air Marshal Hasan Abubakar, ya jadadda bukatar samar da hanyoyin warware kalubalen tsaro da kasashen Afirka ke fuskanta.

 

A cikin wata sanarwa da daraktan hulda da jama’a da yada labarai na NAF, Air Vice Marshal Olusola Akinboyewa, ya fitar, hafsan hafsoshin ya bayyana muhimmancin hadin gwiwa tsakanin shiyya da dabarun hadin gwiwa wajen karfafa karfin jiragen na Afrika da kuma magance barazanar da ake fuskanta.

 

Ya jaddada cewa, inganta hadin gwiwa tsakanin sojojin saman Afrika na da matukar muhimmanci wajen tunkarar kalubalen tsaro da ke kunno kai kamar ta’addanci, tada kayar baya da kuma laifuffukan kasa da kasa.

 

Air Marshal Hasan Abubakar ya lura da cewa taron na nuni ne da jajircewa wajen tabbatar da tsaro, kwanciyar hankali da wadata a Afirka.

 

Ya yi kira da a sabunta alkawari daga dukkan mambobin, yana mai jaddada cewa hadin kai na da matukar muhimmanci wajen cimma manufofin kungiyar.

 

A cewar sanarwar, kungiyar ta AAAF, kungiya ce mai zaman kanta da ba ta siyasa ba, da ta himmatu wajen inganta karfin samar da kariyarar sararin samaniyar Africa da hadin gwiwa tsakanin kasashen Afirka.

 

PR/Usman Sani.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Nijeriya hadin gwiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Kwarewar Kasar Sin Da Ci Gabanta A Fannin Fasaha Na Da Muhimmanci Wajen Inganta Zamanantar Da Afirka

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Da Jamhuriyar Congo Za Su Karfafa Raya Hadin Gwiwar Sin Da Afrika
  • Sin Da Laberiya Sun Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Ta Fuskar Tattalin Arziki Da Fasaha 
  • Jami’an Tsaro A Jihar Kano Na Tarayyar Najeriya Sun Hana Bikin Dabar NA Sallar Bana
  • Kungiyar “White Helmets Ta” A Kasar Siriya Ta Rasha Tallafin Da Take Samu Daga USAID
  • An cafke mutum 19 bayan arangama tsakanin sojoji da ’yan shi’a a Abuja
  • Kwarewar Kasar Sin Da Ci Gabanta A Fannin Fasaha Na Da Muhimmanci Wajen Inganta Zamanantar Da Afirka
  • Tinubu zai sake zama shugaban ƙasa a 2027 — Akpabio
  • Jihad Islami: Ranar Quds Dama Ce Ta Hadin Kai Tsakanin Al’umma
  • Najeriya Da Ghana Sun Jaddada Aniyarrsu  Wajen Kara Fadada Alakarsu A Dukkanin Bangarori
  • Iran, Lebanon, Iraki, Yemen sun fara atisayen hadin gwiwa na goyan bayan Gaza