Leadership News Hausa:
2025-03-29@20:53:09 GMT

Gidauniyar Sarki Salman Ta Rab Tallafin Abinci Ga Mutane 2,450 A Kebbi

Published: 27th, February 2025 GMT

Gidauniyar Sarki Salman Ta Rab Tallafin Abinci Ga Mutane 2,450 A Kebbi

Gidauniyar Sarki Salman ta Saudi Arabiya ta bayar da tallafin kayan abinci ga marasa ƙarfi 2,450 a Jihar Kebbi ta hannun hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA). An gudanar da rabon ne a Birnin Kebbi, inda aka raba buhuhunan shinkafa da wake mai nauyin kilo 25, garin masara kilo 2, da man gyada. An gudanar da rabon kayan ne a ɗakin ajiyar abinci na gwamnatin jihar da ke Bulasa.

Mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Umar Abubakar Tafida, wanda ya wakilci Gwamna Nasir Idris a wajen rabon, ya gode wa gidauniyar bisa tallafin da ta ke bai wa mutanen jihar.

Amurka Da Rasha Sun Kammala Tattaunawar Kawo Ƙarshen Yakin Yukiren A Ƙasar Saudiyya Hajjin 2025: Kamfanin Saudiyya Ya Amince Da Kwangilar Aiki Da NAHCON Bayan Sabunta Yarjejeniya 

Ya ce wannan ba shi ne karo na farko da gidauniyar ke taimakawa ba, yana mai yabawa da kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin su da ƙasar Saudi Arabiya, musamman kan ayyukan jin ƙai da aikin hajji. Gwamnatin jihar ta yaba da rawar da NEMA ta ke takawa wajen rabon tallafin.

Shugabar hukumar NEMA ta ƙasa, Hajiya Zubaida Umar, wadda Hajiya Fatima Kasim ta wakilta, ta ce gidauniyar Sarki Salman ta dauki tsawon lokaci tana bayar da irin wannan tallafi tun daga shekarar 2018 domin taimakawa marasa galihu a Nijeriya. Ta bayyana cewa bayan Kebbi, za a ci gaba da rabon kayan abinci a jihar Adamawa. NEMA ta gode wa gwamnatin tarayya da Gwamnatin Jihar Kebbi bisa haɗin kan da suka bayar wajen ganin an aiwatar da aikin cikin nasara.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

NLC a Zamfara sun Bada Wa’adin Kwanaki 14 a Aiwatar da Mafi Karancin Albashi

Kungiyoyin kwadagon Najeriya NLC da TUC a jihar Zamfara sun bayar da wa’adin kwanaki 14 ga gwamnatin jihar, inda suka bukaci da a kawo karshen kura-kuran da aka samu wajen aiwatar da mafi karancin albashi na N70,000.

 

An sanar da wa’adin ne a wani taron manema labarai a Gusau bayan wani taron gaggawa da kungiyoyin kwadago suka yi.

 

Da yake jawabi a wajen taron, shugaban kungiyar NLC na jihar Zamfara, Malam Sani Halliru, ya bayyana rashin jituwar da ake samu wajen biyan albashin watan Maris a matsayin abin bakin ciki da damuwa ga ma’aikatan gwamnati.

 

“Ya zama dole mu kira wannan taron manema labarai saboda mun ji takaicin yadda gwamnatin jihar ke aiwatar da mafi karancin albashi,” in ji Halliru.

 

Ya kara da cewa tun da farko gwamnatin jihar ta kafa kwamitin da zai sa ido a kan yadda za a aiwatar da sabon albashin tare da tabbatar wa ma’aikata cewa za a fara aiki a watan Maris. Sai dai ya lura cewa albashin watan Maris da aka biya a baya-bayan nan ya gaza yadda ake tsammani.

 

“Wasu ma’aikata sun samu karin Naira 3,000 kacal, yayin da wasu suka samu N4,000, N5,000, ko kuma akalla Naira 7,000. Har ma fiye da haka, an cire wasu ma’aikatan ba bisa ka’ida ba daga cikin albashin ma’aikata.” Ya kara da cewa.

 

Malam Sani Haliru ya kuma bayyana lamarin a matsayin cin amana, ya kuma yi gargadin cewa, idan gwamnati ta gaza magance wadannan matsalolin nan da makonni biyu, kungiyoyin za su dauki mataki.

 

Shi ma da yake jawabi, Shugaban TUC, Sa’idu Mudi, ya koka kan yadda har yanzu Zamfara ce jiha daya tilo da ba ta fara aiwatar da mafi karancin albashi na N70,000.

 

“Dukkan shugabannin kwadago da ma’aikata a jihar sun ji takaicin gazawar gwamnati wajen cika alkawarin da ta dauka.

 

A cewar Mudi sun ji takaicin kwamitin da aka nada domin aiwatar da sabon albashin yaki yin aikin da ya dace.

 

Ya yi zargin cewa da gangan wasu mutane a cikin gwamnati ke yin zagon kasa wajen aiwatar da aikin tare da yin kira ga Gwamna Dauda Lawal da ya kaddamar da bincike kan lamarin tare da daukar matakin da ya dace.

COV/AMINU DALHATU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Jahun Ta Bada Tallafin Noman Rani Ga Manoma 300
  • Jami’an Tsaro A Jihar Kano Na Tarayyar Najeriya Sun Hana Bikin Dabar NA Sallar Bana
  • Kungiyar “White Helmets Ta” A Kasar Siriya Ta Rasha Tallafin Da Take Samu Daga USAID
  • Kisan ‘Yan Arewa 16 A Jihar Edo: Gidauniyar Sir Ahmadu Bello Ta Nemi Adalci
  • Ƙungiyar JNI ta raba wa marayu 50 kayan Sallah a Borno
  • WFP: Yara Miliyan 11 Na Fama Da Karanci Abinci A Nijeriya
  • Duk Da Dokar ‘Yancin Samar Da Abinci: Yara Miliyan 11 Na Fama Da Ƙaranci Abinci A Nijeriya
  • Ina Mafita Game Da Ƙalubalen Ƙarancin Abinci A Nijeriya
  • Za a Fara Cin Moriyar Shirin BEAR III Na UNESCO da Koria Ta Kudu Jihar Kano
  • NLC a Zamfara sun Bada Wa’adin Kwanaki 14 a Aiwatar da Mafi Karancin Albashi