Gidauniyar Sarki Salman Ta Rab Tallafin Abinci Ga Mutane 2,450 A Kebbi
Published: 27th, February 2025 GMT
Gidauniyar Sarki Salman ta Saudi Arabiya ta bayar da tallafin kayan abinci ga marasa ƙarfi 2,450 a Jihar Kebbi ta hannun hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA). An gudanar da rabon ne a Birnin Kebbi, inda aka raba buhuhunan shinkafa da wake mai nauyin kilo 25, garin masara kilo 2, da man gyada. An gudanar da rabon kayan ne a ɗakin ajiyar abinci na gwamnatin jihar da ke Bulasa.
Mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Umar Abubakar Tafida, wanda ya wakilci Gwamna Nasir Idris a wajen rabon, ya gode wa gidauniyar bisa tallafin da ta ke bai wa mutanen jihar.
Amurka Da Rasha Sun Kammala Tattaunawar Kawo Ƙarshen Yakin Yukiren A Ƙasar Saudiyya Hajjin 2025: Kamfanin Saudiyya Ya Amince Da Kwangilar Aiki Da NAHCON Bayan Sabunta YarjejeniyaYa ce wannan ba shi ne karo na farko da gidauniyar ke taimakawa ba, yana mai yabawa da kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin su da ƙasar Saudi Arabiya, musamman kan ayyukan jin ƙai da aikin hajji. Gwamnatin jihar ta yaba da rawar da NEMA ta ke takawa wajen rabon tallafin.
Shugabar hukumar NEMA ta ƙasa, Hajiya Zubaida Umar, wadda Hajiya Fatima Kasim ta wakilta, ta ce gidauniyar Sarki Salman ta dauki tsawon lokaci tana bayar da irin wannan tallafi tun daga shekarar 2018 domin taimakawa marasa galihu a Nijeriya. Ta bayyana cewa bayan Kebbi, za a ci gaba da rabon kayan abinci a jihar Adamawa. NEMA ta gode wa gwamnatin tarayya da Gwamnatin Jihar Kebbi bisa haɗin kan da suka bayar wajen ganin an aiwatar da aikin cikin nasara.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Matar gwamna ta ɗauki nauyin ragon suna da hidimar duk matar da ta haifi ’yan uku a Sakkwato
Uwargidan Gwamnan Sakkwato Hajiya Fatima Ahmad Aliyu ta ɗauki nauyin ragon suna da abinci da kayan barka ga duk wata mata da tahaifi ’yan uku a jihar.
Hahiya Fatima ta sanar da haka ne a ranar Laraba nan a lokacin da ta yi takakkiya takanas zuwa garin Ƙaurar Yabo da ke Ƙaramar Hukumar Yabo domin kai ragunan suna da kayan barka da na suna ga wata mai jego mai suna Malama Bela’u, wadda ta haifi ’yan uku a garin.
Daga cikin kayan da ta kai wa mai jego kyauta, har da buhun abinci goma da akwatunan tufafi da tsabar kudi Naira dubu dari biyar.
A bayanin da mataimaka wa gwamna kan harkokin kafofin sada zumunta, Nasir Bazza, ya fitar, ya ce mutanen ƙauyen sun yi farin cikin ganin matar gwamna a garin, wanda shi ne karo na farko da suka ga matar gwamna a yankin nasu.
Ya ce matar gwamna ta yi alkawalin ci gaba da bayar da irin wannan tallafi ga duk wata mata da Allah ya albrkace ta da samun karuwar ’yan uku a lokaci guda a jihar.