Aminiya:
2025-03-29@20:23:10 GMT

Boko Haram ta ƙona wuraren ibada da gidaje a Adamawa

Published: 27th, February 2025 GMT

Mayaƙan Boko Haram sun kai hari a cikin dare inda suka ƙona wuraren ibada da gidaje da makarantu da shaguna a ƙauyen Kwapre da ke yankin Sabuwar Yadul a Ƙaramar Hukumar Hong ta Jihar Adamawa.

Gabanin Sallar Isha’ a ranar Talata ne mayaƙan suka far wa yankin da hari, inda suka yi ta cin karensu babu babbaka.

Mazauna sun bayyana cewa maharan sun ƙona wuraren ibada da makarantu da gidaje da shaguna sannan suka sace dukiyoyin jama’a.

Mai unguwar kauyen Kwampre da Joel Kulaha, ya tabbatar da aukuwar lamarin, amma ya ce ba a samu asarar rai ba.

NAJERIYA A YAU: Halin da jama’a za su shiga idan Kamfanin Kaduna Electric ya ƙi sauraren ma’aikatansa Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N860 a Legas

Ya bayyana cewa mazauna yankin sun tsare bayan farmaki da ’yan ta’addan suka kai musu.

“Mun samu tsira da rayukanmu, amma mu rasa duk wani abu da muka mallaka,” in ji shi, yana mai cewa babu dalilin harin da aka kawo musu.

Rahotanni sun bayyana cewa sojojin da aka girke a yankin Garaha da ke kusa da wurin sun kawowa al’ummar ɗauki, inda suka yi artabu tare da fatattakar maharan.

Sai dai mazauna na zargin cewar jami’an tsaron sun yi jinkirin zuwa, shi ya sa maharan suka yi ɓarna fiye da kima.

Wakilinmu ya yi ƙoƙarin zantawa da kakakin Birget na 23 na rundunar Sojan Najeriya, A. S. Adewunmi, amma jami’in bai amsa kiran waya ko rubutaccen sakon da aka aika masa ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hari mayaƙa

এছাড়াও পড়ুন:

Ana Gudanar Da Tarukan Ranar Quds Ta Duniya A Wannan Juma’a

A safiyar yau ne aka fara gudanar da jerin gwano na ranar Qudus ta duniya a duk fadin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, inda aka samu halartar jama’a da dama karkashin taken “Muna ci gaba da cika alkawarin da muka dauka.” Mahalarta taron za su yi tattaki ne daga masallatai da manyan filaye a birane da kauyukan kasar zuwa wuraren da ake gudanar da Sallar Juma’a.

A birnin Mashhad da ke gabashin Iran, tun da sanyin safiya ne aka fara gudanar da jerin gwano a wani bangare na bikin na shekara-shekara.

A halin da ake ciki dai jama’a a birnin Tehran sun fara taruwa daga wurare daban-daban a kan titin juyin juya hali domin tunawa da wannan rana. A cewar wakilin Al Mayadeen a Tehran, “Biranen 900 na Iran za su halarci bukukuwan ranar Qudus.”

Jagoran juyin juya halin Musulunci a Iran Sayyed Ali Khamenei ya bayyana cewa tattakin ranar Kudus ta duniya da za a yi a ranar Juma’a da yardar Allah za ta kasance daya daga cikin mafificiyar masifu, mafi daukaka da daraja.

A cikin wani sakon da ya aike ta gidan talabijin a daren jiya Alhamis, jagoran ya bayyana cewa, wannan rana a ko da yaushe wata alama ce ta hadin kai da karfin al’ummar Iran, yana mai bayyana yadda tattakin ke nuni da cewa al’ummar kasar na da tsayin daka da tsayin daka kan muhimman manufofinta na siyasa da na siyasa, da kuma kin yin watsi da kasar Falasdinu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin da ya sa nake jin daɗin yadda Tinubu yake tafiyar da gwamnatinsa — Buhari
  • Dalilin da Aminu Bayero ba zai iya jagorantar hawan Sallah ba — Kurawa
  • Wadanda Iftila’in Tankar Mai Ya Sha A Jigawa Sun Sami Naira Miliyan 4 Kowannensu
  • Rikici ya ɓarke bayan wata mata ta mari ɗan sanda a Saudiyya
  • Maduro Ya Bayyana Sakataren Harkokin Wajen Amurka Da Cewa Wawa Ne
  • Gwamnatin Kaduna Ta Jadadda Kudurin Ta Wajen Samarda Tsaftatacen Ruwan Sha Ga Al’umma 
  • Manyan Amfanin Gona Biyar Da Ya Kyautu Manoma Su Zuba Hannun Jari A 2025
  • Yadda kisan ’yan Arewa 16 a Edo ya tayar da ƙura a faɗin Nijeriya
  • An Kama Wanda Ake Zargi Da Kashe Mai PoS A Adamawa
  • Ana Gudanar Da Tarukan Ranar Quds Ta Duniya A Wannan Juma’a