Sarkin Musulmi ya ba da umarnin dubin watan Ramadan
Published: 27th, February 2025 GMT
Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar ya bayar da umarni ga jama’a da su fara duban jaririn watan Ramadan daga ranar Jumu’a 29 ga watan Sha’aban, 1446 Bayan Hijira, wanda ya yi daidai da 28 ga watan Fabrairu, 2025.
Shugaban Kwamitin Bayar da Shawara kan Harkokin Addini a Fadar Sarkin Musulmi, Wazirin Sakkwato, Farfesa Sambo Wali Junaidu ne ya sanar da hakan a wata takarda da ya raba wa manema labara.
Wazirin Sakkwato ya ce duk wanda ya samu ganin jinjinrin watan Ramadan ya sanar da hakimi ko uban ƙasar da ke kusa da shi.
Daga nan ne za a kai maganar ga Sarkin musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar.
Ya roƙi Allah Ya taimake su a cikin wannan aikin da suke yi na addini.
Ramadan shi ne wata na tara a kalandar Musulunci, kuma al’ummar Musulmi na azumtar sa baki ɗaya.
Azumin Ramadan shi ne ka uku a cikin ginshikan addinin Musulunci guda biyar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Azumin Ramadan Ramadan Sarkin Musulmi Sarkin Musulmi
এছাড়াও পড়ুন:
Hizbullah Ta Yi Allawadai Da Keta Hurumin Masallacin Kudus Da ‘Yan Sahayoniya Su Ka Yi
Kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ta fitar da bayani da ya kunshi yin Allawadai da keta hurumin masallacin kudus da ‘yan sahayoniya su ka yi a cikin kwanaki uku a jere.
“Yan sahayoniyar dai sun rika shiga cikin harabar masallacin na Kudus, suna yin ibadunsu na yahudanci, tare da kariyar ‘yan sandan HKI.
Kungiyar ta Hizbullah ta kuma ce; Abinda ‘yan sahayoniyar suke yi nuna kiyayya ne, da keta hurumin masallacin kudus.
Bugu da kari sanarwar ta kara da cewa; Abinda ;yan sahayoniyar suke yi, ya isa bakantawa musulmi al’ummunsu da gwmanatocinsu, ya kuma sa su yunkurawa domin hana ci gaba da abinda yake faruwa.
Hizbullah ta kuma ce; Al’ummarmu ta larabawa da musulmi tana da cikakkiyar masaniya akan bukatar a daga murya da karfi da kuma yin dukkanin abinda ya kamata domin fuskantar wannan keta hurumin, saboda yin shiru yana kara karfafa abokan gaba akan abinda suke yi a cikin Kudus, yammacin kogin Jordan, Syria da kuma Yemen.
Bayanin na kungiyar Hizbullah ya kuma yi kira ga kungiyoyin kasashen musulmi da na larabawa da kuma cibiyoyin addini da malamai ma ‘yantattu a duk duniya da su yunkura da sauri, su kuma dauki nauyin da ya rataya a wuyansu na tarihi.