Sarkin Musulmi ya ba da umarnin dubin watan Ramadan
Published: 27th, February 2025 GMT
Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar ya bayar da umarni ga jama’a da su fara duban jaririn watan Ramadan daga ranar Jumu’a 29 ga watan Sha’aban, 1446 Bayan Hijira, wanda ya yi daidai da 28 ga watan Fabrairu, 2025.
Shugaban Kwamitin Bayar da Shawara kan Harkokin Addini a Fadar Sarkin Musulmi, Wazirin Sakkwato, Farfesa Sambo Wali Junaidu ne ya sanar da hakan a wata takarda da ya raba wa manema labara.
Wazirin Sakkwato ya ce duk wanda ya samu ganin jinjinrin watan Ramadan ya sanar da hakimi ko uban ƙasar da ke kusa da shi.
Daga nan ne za a kai maganar ga Sarkin musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar.
Ya roƙi Allah Ya taimake su a cikin wannan aikin da suke yi na addini.
Ramadan shi ne wata na tara a kalandar Musulunci, kuma al’ummar Musulmi na azumtar sa baki ɗaya.
Azumin Ramadan shi ne ka uku a cikin ginshikan addinin Musulunci guda biyar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Azumin Ramadan Ramadan Sarkin Musulmi Sarkin Musulmi
এছাড়াও পড়ুন:
Aminu Bayero ya soke hawan Sallah
Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya sanar da soke bukukuwan Sallah na bana, saboda bukatar tabbatar da zaman lafiya da tsaro a jihar.
A wata sanarwa da aka fitar, Sarkin ya bayyana takaicinsa kan matakin amma ya jaddada cewa, tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi shi ne babban abin da ya sa a gaba.
Sarkin ya ce, “Bisa umarnin da jama’a suka ba mu da kuma jajircewar da muka yi na ba su kariya, mun ga ya dace mu janye duk wani shiri da aka yi na bukukuwan Sallah bisa la’akari da halin da ake ciki.”
Ya kara da cewa, tuntubar da aka yi da manyan malaman addini da sauran masu ruwa da tsaki sun yi tasiri a kan shawarar.
Ya kuma jaddada cewa, duk da cewa bikin Sallah al’ada ce mai kima, bai kamata ta zo da rashin zaman lafiya da kwanciyar hankali ba.
Name(required) Email(required) Website MessageSubmit