Aminiya:
2025-04-19@21:17:21 GMT

An shiga ruɗani bayan Obasa ya koma majalisar Legas da ’yan sanda

Published: 27th, February 2025 GMT

An shiga ruɗani bayan Tsohon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Legas, Mudashiru Obasa, ya koma majalisar tare da rakiyar ’yan sanda.

An sauke Obasa daga muƙaminsa a ranar 13 ga watan Janairu kan zargin yin amfani da ofis ɗinsa ba daidai ba.

An yi wa mutane damfarar Naira biliyan 52 ta banki —NIBSS Boko Haram ta ƙona wuraren ibada da gidaje a Adamawa

An maye gurbinsa da Mojisola Meranda, wanda hakan ya haifar da rarrabuwar kai a majalisar da kuma jam’iyyar APC mai mulki a Jihar.

Rahotanni sun nuna cewa an matsa wa Meranda da ta sauka daga muƙaminta, bayan da ake zargin cewa Shugaba Bola Tinubu bai gamsu da sauke Obasa daga muƙaminsa ba.

A safiyar ranar Alhamis, labari ya bayyana cewa an janye wa Meranda jami’an tsaron da ke ba ta kariya.

A gefe guda guma an mayar wa jami’an da za su ba shi kariya, alamar da ke nuna ana shirin dawo da shi kan muƙaminsa.

Wata majiya ya shaida wa Aminiya cewa Obasa ya shiga zauren majalisa tare da ’yan sanda, yana ƙoƙarin shiga ofishin kakakin majalisar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jami an Tsaro Majalisar Dokoki Ruɗani

এছাড়াও পড়ুন:

UEFA: Wasan Arsenal Da Real Madrid Ya Haddasa Rikici A Tsakanin Magoya Bayan Kungiyoyin A Kano

An tabbatar da cewa, tashin hankalin ya barke ne jim kadan bayan da alkalin wasa ya busa tashi daga wasan, kawo yanzu dai babu wata sanarwa a hukumance da rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta fitar har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto a safiyar ranar Alhamis, kuma kawo yanzu babu tabbacin ko an samu raunika a yayin rikicin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi
  • ’Yan sanda sun ceto ɗalibai 10 sun kashe ɗan bindiga a Edo
  • An buɗe wa jami’an NDLEA wuta a Abuja
  • Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.
  • ’Yan sanda sun ceto ɗalibai 10 sun lashe ɗan bindiga a Edo
  • Dokar-ta-baci: Shugaban Majalisar Wakilai Ya Gargadi Kantoman Ribas
  • Bukatar Kawo Karshen Mamayar Da Kamaru Ke Yi Wa Yankunan Nijeriya
  • Manchester Ta Kai Zagayen Semi Final A Europa Bayan Doke Lyon
  • UEFA: Wasan Arsenal Da Real Madrid Ya Haddasa Rikici A Tsakanin Magoya Bayan Kungiyoyin A Kano
  • Majalisar Dokokin Zamfara Ta Dawo da Dan Majalisa Basko da Aka Dakatar