Aminiya:
2025-02-27@19:10:04 GMT

An shiga ruɗani bayan Obasa ya koma majalisar Legas da ’yan sanda

Published: 27th, February 2025 GMT

An shiga ruɗani bayan Tsohon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Legas, Mudashiru Obasa, ya koma majalisar tare da rakiyar ’yan sanda.

An sauke Obasa daga muƙaminsa a ranar 13 ga watan Janairu kan zargin yin amfani da ofis ɗinsa ba daidai ba.

An yi wa mutane damfarar Naira biliyan 52 ta banki —NIBSS Boko Haram ta ƙona wuraren ibada da gidaje a Adamawa

An maye gurbinsa da Mojisola Meranda, wanda hakan ya haifar da rarrabuwar kai a majalisar da kuma jam’iyyar APC mai mulki a Jihar.

Rahotanni sun nuna cewa an matsa wa Meranda da ta sauka daga muƙaminta, bayan da ake zargin cewa Shugaba Bola Tinubu bai gamsu da sauke Obasa daga muƙaminsa ba.

A safiyar ranar Alhamis, labari ya bayyana cewa an janye wa Meranda jami’an tsaron da ke ba ta kariya.

A gefe guda guma an mayar wa jami’an da za su ba shi kariya, alamar da ke nuna ana shirin dawo da shi kan muƙaminsa.

Wata majiya ya shaida wa Aminiya cewa Obasa ya shiga zauren majalisa tare da ’yan sanda, yana ƙoƙarin shiga ofishin kakakin majalisar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jami an Tsaro Majalisar Dokoki Ruɗani

এছাড়াও পড়ুন:

Ya daɓa wa yayansa wuƙa saboda Naira 700

Wani matashi ɗan shekara 32 ya soka wa ɗan uwansa wuƙa ya saboda Naira 700 a Unguwar Zara da ke Yankin Babban Birnin Tarayya.

Wani shaida a unguwar ya bayyana cewa lamarin ya faru ne bayan wanda ake zargin ya kutsa ɗakin yayan nasa ya ɗauke masa Naira 700 daga aljihunsa.

Ana zargin wanda a ya yi aika-aikan ya shiga dakin ne bayan wan nasa ya tafi Sallar Isha’i

Bayan ya dawo bai ga kuɗin ba, ya yi zargin ƙanin nasa da ɗaukar, ya bi sahunsa, inda ya riske shi a wata mashaya ya je sayen tabar wiwi.

Ba ni lokacin cacar baka da El-Rufai —Nuhu Ribadu NAJERIYA A YAU: Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi?

A nan ne taƙaddama ta ɓarke a tsakaninsu, inda ƙanin ya zaro wuƙa ya daɓa masa, sannan ya tsere bayan ya ga ’yan banga za su kawo ɗauki.

Sanusi ya ce ’yan banga da sauran mutane ne suka kai wan nasa asibiti.

Wani ɗan banga, Bala Suleiman, ya bayyana cewa ganin su ne ya sa wanda ake zargin ya tsere.

Ya ƙara da cewa wanda ake zargin sanannen ɗan shaye-shaye, kuma a baya ya taɓa kai wa wasu mutum uku farmaki.

Ya ce suna ci gaba da bin sawunsa, kuma wanda aka taka wa wukar yana samun sauƙi a asibiti.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Labarin Bukar, Malamin Da Ya Shafe Watanni 20 Ba Tare Da Albashi Ba A Borno
  • Majalisar Dattijan Aljeriya Ta Soke Duk Wata Hulda Da Majalisar Dattijan Faransa
  • Messi Zai Fuskanci Hukunci A Gasar MLS Ta Kasar Amurka
  • Nebenzia : Hare-haren Sojojin Isra’ila a Lebanon da Syria na kara dagula lamura a yankin
  • Babu hannun Naira Marley a mutuwar Mohbad — Kotu
  • Dan kwallon Najeriya ya mutu bayan fadowa daga bene a Uganda
  • Mutum 7,000 Suka Mutu A Rikicin Gabashin Kwango Tun Daga Watan Janairu
  • Magidanci ya sari matarsa da adda har lahira
  • Ya daɓa wa yayansa wuƙa saboda Naira 700