Aminiya:
2025-05-07@08:10:50 GMT

Zulum ya rage adadin tallafin rabon abinci da kashi 90 a Borno

Published: 27th, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya sanar da rage kashi 90 na tallafin rabon kayan abinci don ƙarfafa dogaro da kai a tsakanin mazauna jihar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin da yake ƙaddamar da rabon kayan abinci ga magidanta 25,000 gabanin watan Ramadan a Maiduguri, Jere da sauran sassan jihar.

Helikwaftan farko ƙirar Najeriya zai fara aiki —NASENI Sarkin Musulmi ya ba da umarnin dubin watan Ramadan

A cewar Zulum, gwamnatin jihar za ta ba da fifiko ga hanyoyin samar da ci gaba na tsawan lokaci a kan matakan agaji na gajeren lokaci kamar rabon tallafin abinci.

Ya kuma bayyana irin gagarumin jarin da gwamnatinsa ta yi wajen tallafa wa manoma sama da miliyan ɗaya da muhimman kayayyakin amfanin gona kamar irin su iri, taki, famfunan ban-ruwa, maganin ƙwari da magungunan kashe ciyawa.

“Wannan dabarar ba kawai za ta inganta dogaro da kai ba ce har ma da rage kashe kuɗaɗen gwamnati,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, rabon kayan tallafin zai taƙaita ne ga ƙananan hukumomin jihar guda biyu kawai daga cikin 27  a shekarar 2025 saboda ƙalubalen da suke fuskanta.

“Ƙananan Hukumomin da za su sami tallafin abinci a shekara mai zuwa su ne: Ngala da Kala-Balge saboda yanayi na musamman.

“Waɗannan yankuna sun fuskanci mummunar ɓarna a gonakinsu daga giwaye kuma sun fuskanci ambaliyar ruwa. Don haka, a shekarar 2025, gwamnatin Jihar Borno za ta samar da kayayyakin tallafin abinci ga Ngala da Kala-Balge kaɗai,” inji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Umara Zulum Umara

এছাড়াও পড়ুন:

Ya kamata a zuba jari a harkar noman rani — Zulum

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara ya bukaci Hukumar Raya Yankin Tafkin Chadi (CBDA) da ta sanya hannunjari sosai a fannin noman rani a kewayen yankin Tafkin Chadi, domin bunkasa wadatar abinci da kuma farfado da tattalin arziki a fadin jihar da kuma yankin Arewa maso Gabas.

Gwamna Zulum ya yi wannan kiran ne a lokacin da shugaban hukumar Farfesa Abdu Dauda Biu ya kai masa ziyarar ban girma a gidan gwamnati da ke Maiduguri.

Wa zai cire wa Real Madrid kitse a wuta? Mai shekara 92 ya shiga gasar Gudun Fanfalaƙi karo na 30 a jere

Da yake karin haske kan yadda ake noma a yankin, gwamnan ya bayyana cewa, gabar Tafkin Chadi, musamman yankunan da suka hada da Kirenowa da Marte da Gamborun Ngala da Baga suna da albarkatu masu yawa na ruwan karkashin kasa da kuma filayen noma da ya dace da noman rani.

“Ina so in ja hankalinku game da kasancewar ruwan kasa mai yawa a gabar Tafkin Chadi. Kada mu dogara ga ruwa sama kawai,” in ji Zulum.

Ya kara da cewa, “kwanan nan na aika da tawagar bincike don gano gaskiya zuwa Gamborun Ngala, kuma tawagar ta tabbatar mana da samun albarkatun ruwan karkashin kasa, wadanda za mu iya amfani da su wajen noman rani ta hanyar ban-ruwa.”

Gwamna Zulum ya kuma bayyana cewa, gwamnatin jihar ta ba da kimanin Naira biliyan 2 domin noma hekta 1,000 na gonaki ta hanyar amfani da na’urar noman rani mai amfani da hasken rana a garin Baga.

Sannan an ware ƙarin Naira biliyan 1.5 domin gudanar da irin wadannan ayyuka a garuruwan Gamborun Ngala da Marte, wadanda dukkansu ke gab da kammaluwa.

“A kokarinmu na farfado da shirin noman rani na a Gabar Tafkin Chadi ta Kudu, a halin yanzu muna noman fili mai fadin hekta 1,000 a karkashin aikin noman rani na Baga a kan kudi kimanin Naira biliyan 2.

Bugu da kari, muna samar da hekta 200,000 a Gamboru da kuma wata hekta 200,000 na samar da wutar lantarki ta Lamboru ta hanyar amfani da tsarin ban-ruwa, don farfado da ayyukan noma a fadin yankin,” in ji zulum.

Farfesa Zulum ya ci gaba da cewa, gwamnatinsa ta yi nasarar haka rijiyoyi kusan 3,000 a Damasak da ke Karamar Hukumar Mobbar, wanda hakan ya bai wa manoma damar yin noma a fili mai tsawon kilomita 16, matakin da ya bullo da hanyar noman ruwan karkashin kasa a yankin da a baya ba a saba da yin irin sa ba.

Gwamnan ya yi alkawarin ci gaba da hada kai da hukumar CBDA, domin fadada noman a Ngala da Damasak da New Marte da samar da ababen more rayuwa ga wadanda suka dawo da kuma tabbatar da dorewar samuwar abinci.

Ya kuma bayyana aniyar gwamnatin jihar na tallafawa wajen farfado da Tashar Famfunan Ruwa ta Chadi Basin Kirenowa, inda ya ce ana kokarin kafa bataliyar soji a yankin domin inganta tsaro.

“A matsayinmu na gwamnati, za mu so sanin inda za mu iya shiga saboda abubuwan da za a iya samu suna nan. Ina tuntubar Shugaban kasa da shugabannin sojoji kan yiwuwar kafa bataliyar soji a Kirenowa da nufin kare tashar famfon,” in ji Zulum.

A nasu jawabin shugaban hukumar Farfesa Abdu Dauda Biu da Manajin Darakta, Alhaji Tijjani Tumsa sun sanar da gwamnan cewa, an kafa sabuwar hukumar ce a ranar 13 ga watan Disamba 2024.

Sun bayyana cewa, sun ziyarci muhimman wurare da ke karkashin kulawarsu, ciki har da Madatsar Ruwa ta Alau, sun kuma yaba wa Gwamna Zulum kan yadda yake gudanar da ayyukanta.

Shugabancin Hukumar ta CBDA ya yi alkawarin hada kai da gwamnatin jiha don aiwatar da ayyukan da suka shafi noman rani da kiwon dabbobi da kamun kifi.

Sun kuma nemi goyon bayan gwamnan don ganin an kammala gyaran madatsar ruwa ta Alau a kan lokaci, wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da shi a kwanakin baya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dattawa ta kafa kwamitin lura da gwamnan riƙo na Jihar Ribas
  • Gwamnan Bauchi Ya Yi Allah-wadai Da Kisan ‘Yan Banga A Alkaleri
  • Matashi ya kashe mahaifinsa da adda a Jigawa
  • Zulum Ya Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira 6,000 Garuruwansu A Borno
  • Xi Jinping Ya Ba Da Umarnin Ceto Mutane Daga Hadarin Jiragen Ruwa
  • Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi
  • Kada ku karaya da shigo da abinci daga ƙasar waje — IAR
  • Abin da ya hana ni cika alƙawarin da na yi wa ma’aikata — Gwamnan Sakkwato
  • Gwamnan California: California Za Ta Ci Gaba Da Bude Kofa Ga Sin Domin Gudanar Da Kasuwanci
  • Ya kamata a zuba jari a harkar noman rani — Zulum