HausaTv:
2025-03-30@18:31:00 GMT

Amnesty: Isra’ila Ta Kori Falasdinawa 40,000 Daga Yammacin Kogin Jordan

Published: 27th, February 2025 GMT

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Amnesty International” ta kira yi Isra’ila da ta gaggauta dakatar da siyasar amfani da karfi na yi wa Falasdinawa karfa-karfa a yammacin kogin Jordan. Hakan nan kuma ta yi kira ga HKI da ta daina ayyukan da za su iya zama azabtar da al’umma kaco kau.

Kungiyar ta kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa ta kuma bayyana cewa, irin wannan siyasar da Isra’ilan take amfani da ita, ta tilasata wa Falasdinawa 40,000 yin hijira daga yammacin kogin Jordan.

Hukumar ta “Amnesty” ta sanar a yau Alhamis cewa; Falasdinawa mazauna “Budhum” a Musafir suna fuskantar hatsarin korarsu a kurkusa saboda yadda ‘yan share wuri zauna suke kai musu hare-hare a karkashin kariyar hukumar ‘yan sahayoniya. Har ila yau ana rushewa Falasdinawan gidajensu da kuma takura musu matuka idan suna son shiga wurin wasu yankunan na Falasdinu.

Wata daga cikin matsalolin da Falasdinawan suke fuskanta kamar yadda “Amnesty” ta  bayyana, ita ce yadda Isra’ila take gina sabbin matsugunan ‘yan share wuri zauna.

 HKI tana son korar Falasdinawa daga yammacin kogin Jordan da kuma Gaza, kuma tana samun goyon bayan gwamnatin Amurka ta Donald Trump.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Karamar Hukumar Jahun Ta Karrama Hakimai Da Limamai Da Kayan Sallah

Shugaban Karamar Hukumar Jahun dake Jihar Jigawa, Alhaji Jamilu Muhammad Danmalam ya kaddamar da rabon kayan sallah da kuma kudin dinki ga al’ummar yankin.

 

A jawabinsa wajen bikin da aka gudanar a garin Jahun, shugaban Karamar Hukumar yace Hakimai na gundumomin Jahun da Aujara da Gunka da Kadawawa da Limaman masalatan juma’a 79 na yankin za su amfana da kayan sallah da kuma kudin dinki.

Jamilu Muhammad Danmalam ya bayyana rashin Jin dadinsa bisa yadda ake mantawa da iyayen kasa da Malaman Addini a irin wannan lokacin da ya kamata a taimake su.

 

Ya ce yana daya daga cikin kudurorinsa na shigo da kowanne bangare na al’umma cikin tsarin shugabancinsa dan kowa ya anfana.

Danmalam ya ce a wannan wata na Ramadan karamar hukumar ta tallafawa masu bukata ta musamman da marayu da masu karamin karfi da shugabannin jam’iyyar APC da ma’aikatan gwamnati da kuma mata da maza.

 

Ya kara da cewar kowanne hakimi ya sami dinkin sallah na shadda mai dauke da shakwara da jamfa da wando, hade da kudin abincin sallah.

A jawabin sa, daya daga cikin limaman yankin Mallam Yahuza Gabari yace a tarihin Karamar Hukumar Jahun ba’a taba samun shugaban da ya kula da limamai da shugabannin al’umma irin shugaban Karamar Hukumar na yanzu ba.

 

Wasu daga cikin wadanda suka anfana da tallafin sun yabawa shugaban Karamar Hukumar bisa tagomashin da suka samu.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wuta
  • Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Miji ya kama matarsa da kwarto ta na’urar drone
  • Hamas A Gaza Ta Amince Da Kafa Gwamnatin Hadin Kan Falasdinawa, Amma Makamanta Jan Layi Ne
  • Yau Lahadi Ce Take Salla A Kasashen Larabawa Da Dama
  • Karamar Hukumar Jahun Ta Karrama Hakimai Da Limamai Da Kayan Sallah
  • Wani Jami’in Leken Asirin HKI Ya Bukaci Kasashen Afirka Su Taimaka Su Karmi Falasdinawan Da Za;a Kora Daga Gaza
  • Abubuwan Da Za Su Iya Kawo Cikas Ga Bukukuwan karamar Sallah
  • Jihad Islami: Ranar Quds Dama Ce Ta Hadin Kai Tsakanin Al’umma
  • Yadda ake fitar da Zakkar Kono