HausaTv:
2025-02-27@21:28:14 GMT

Amnesty: Isra’ila Ta Kori Falasdinawa 40,000 Daga Yammacin Kogin Jordan

Published: 27th, February 2025 GMT

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Amnesty International” ta kira yi Isra’ila da ta gaggauta dakatar da siyasar amfani da karfi na yi wa Falasdinawa karfa-karfa a yammacin kogin Jordan. Hakan nan kuma ta yi kira ga HKI da ta daina ayyukan da za su iya zama azabtar da al’umma kaco kau.

Kungiyar ta kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa ta kuma bayyana cewa, irin wannan siyasar da Isra’ilan take amfani da ita, ta tilasata wa Falasdinawa 40,000 yin hijira daga yammacin kogin Jordan.

Hukumar ta “Amnesty” ta sanar a yau Alhamis cewa; Falasdinawa mazauna “Budhum” a Musafir suna fuskantar hatsarin korarsu a kurkusa saboda yadda ‘yan share wuri zauna suke kai musu hare-hare a karkashin kariyar hukumar ‘yan sahayoniya. Har ila yau ana rushewa Falasdinawan gidajensu da kuma takura musu matuka idan suna son shiga wurin wasu yankunan na Falasdinu.

Wata daga cikin matsalolin da Falasdinawan suke fuskanta kamar yadda “Amnesty” ta  bayyana, ita ce yadda Isra’ila take gina sabbin matsugunan ‘yan share wuri zauna.

 HKI tana son korar Falasdinawa daga yammacin kogin Jordan da kuma Gaza, kuma tana samun goyon bayan gwamnatin Amurka ta Donald Trump.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

LEADERSHIP HAUSA Ta Bayyana Waɗanda Suka Yi Nasara A Gasar Gajerun Labaran Soyayya

Waɗanda Suka Yi Nasara

1. Aliyu Usman Adam – Matsayi na Ɗaya

Aliyu Usman Adam, ɗan asalin Zariya, Jihar Kaduna, an haife shi a shekarar 1984. Ya kammala karatunsa na firamare da sakandare a Zariya, sannan ya samu digiri a harshen Hausa daga Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya, a 2008. Bayan hidimar ƙasa a Jihar Edo, ya yi aiki a kamfanin SAN Yoghurt da kuma Alhuda Center School daga 2011 zuwa 2014.

A 2014, Aliyu ya koma aikin jarida, inda ya yi aiki da jaridar RARIYA a Abuja har zuwa 2017. A halin yanzu, shi ne Manajan shirye-shirye (Content Manager) a Nishadi TV Abuja. Yana da mata da ‘ya’ya biyu.

2. Zainab Muhammad (Indian Girl) – Matsayi Na Biyu

Zainab Muhammad, wacce aka fi sani da “Indian Girl,” ‘yar asalin ƙaramar hukumar Dala ce a Kano. Ta kammala firamare da sakandare a Kano, tare da burin ci gaba da karatun jami’a a nan gaba.

Zainab tana da ƙwazo a ɓangaren ilimin addinin Musulunci, kuma tana amfani da kafafen sada zumunta wajen ilmantarwa da faɗakarwa. A halin yanzu tana da tarin masoya saboda rubuce-rubucenta masu ƙayatarwa da gina al’umma.

3. Mujaheed Nuhu Yusuf (Mujaheed Matashi) – Matsayi Na Uku

Mujaheed Nuhu Yusuf, wanda aka fi sani da Mujaheed Matashin marubuci ne a fagen wasan kwaikwayo kuma mawaki daga Kano. Ya wallafa littattafai biyu na waƙoƙi, ciki har da Philosophy Mysterious Pen, wanda ya wallafa tare da marubuci Haiman Ra’ees.

Mujaheed shi ne shugaban ƙungiyar marubuta Ruhin Adabi, kuma yana wallafa rubuce-rubucensa a shirin Bakandamiya Hikaya da kuma shafinsa na Facebook.

Wannan gasa ta ƙara tabbatar da aniyar LEADERSHIP HAUSA na bunƙasa haɗaka da ƙirƙirar rubutu a cikin al’ummar Hausawa.

Jaridar na shirin ci gaba da shirya irin waɗannan gasar domin ƙarfafa sha’awar adabi da kuma ƙarfafa dangantaka da masu karatu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano ta nemi Tinubu ya kori Aminu Bayero daga fadar Nassarawa
  • Isra’ila Ta Saki Fursunonin Falasdinawa Da Dama
  • Masar Ta Yi Watsi Da Shawarar Cewa Ta Karbi Ragamar Gaza Na Wucin Gadi
  • Majalisar Dattijan Aljeriya Ta Soke Duk Wata Hulda Da Majalisar Dattijan Faransa
  • An Cimma Matsaya Kan Sakin Fursunonin Falasdinawa 206 Da Isra’ila Ta Jinkirta
  • DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa
  • Manoman tumatir na tafka asara saboda faɗuwar farashi
  • LEADERSHIP HAUSA Ta Bayyana Waɗanda Suka Yi Nasara A Gasar Gajerun Labaran Soyayya
  •  HKI: Hamas Ta Sake Gina Kanta A Arewacin Gaza