Aminiya:
2025-04-19@08:47:32 GMT

Kotu ta yanke wa matashi ɗaurin wata 6 kan satar kaza

Published: 27th, February 2025 GMT

Wata kotun majistare da ke zamanta a Ago Iwoye, Jihar Ogun, ta yanke wa wani matashi ɗan shekara 21, Adebanjo Segun, hukuncin ɗaurin watanni shida a gidan yari bisa samunsa da laifin satar kaza.

Jami’in hulɗa da jama’a na Hukumar tsaro ta Civil Defence , Dyke Ogbonnaya ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba.

An ce an fara samun matsalar ne a ranar Laraba, 19 ga Fabrairu, 2025, kan Adebanjo mai shekara 21 a lokacin da aka kama shi da laifin satar kaza.

Zulum ya rage adadin tallafin rabon abinci da kashi 90 a Borno An shiga ruɗani bayan Obasa ya koma majalisar Legas da ’yan sanda

Ogbonnaya ya bayyana cewa, “Bayan an yi nazari sosai kan lamarin tare da kammala bincike, an gano cewa wanda ake tuhuma ya aikata irin wannan laifin a wani lokaci a watan Disambar 2024 inda aka yi masa afuwa a matsayin wanda ake zato da ya yi laifin farko.

“Saboda bayyana laifin da ya aikata a baya, an gurfanar da shi a gaban Kotun Majistare ta Ago-Iwoye kan tuhume-tuhumen da ya shafi sashe na 430 na dokokin manyan laifuka na Jihar Ogun, Nijeriya 2006, a ranar 20 ga Fabrairu, 2025.

“Bayan ya amsa laifinsa a gaban Alƙali ​​O.F. Adeduntan, an same shi da laifin kuma  kotun ta yanke masa hukuncin ɗaurin watanni shida a gidan yari.”

Hakazalika, an kuma yanke wa wani Kazeem Tobi mai shekara 20 hukuncin ɗaurin watanni shida a gidan yari bisa samunsa da laifin satar janareta na Elepaƙ wanda kuɗinsa ya kai kusan N120,000 kacal.

An ce an sake gurfanar da Tobi a ranar Talata, 4 ga watan Fabrairu, 2025, kuma bayan da aka yi nazari sosai a kan lamarin, an gurfanar da shi a gaban Kotun Majistare ta Ago-Iwoye kan tuhume-tuhume biyu da suka shafi haɗa baki wajen aikata laifi da kuma mallakar wani abu da ake zargin an sace.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gidan Yari satar kaza

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe Mutane 7 A Yayin Da ‘Yan Ta’adda Suka Ƙaddamar Da Wani Sabon Hari A Adamawa

An tabbatar da mutuwar mutane bakwai a wani sabon harin da ‘yan ta’adda suka kai a kauyen Garaha Lar da ke jihar Adamawa. Shugaban karamar hukumar Hong, Honarabul Usman Wa’aganda ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa, wani mazaunin garin ya ɓata yayin da maharan suka lalata gidaje da kadarori. An Gudanar Da Harkokin Cudanya Da Musayar Al’adu Tsakanin Sin Da Malaysia A Birnin Kuala Lumpur  Jigawa Za Ta Zama Cibiyar Binciken Lafiya Nan Ba Da Jimawa Ba – Gwamna Namadi Wa’aganda ya kuma bayyana cewa, wani Ɗan banga na yankin ya mutu bayan da wani bam ya tashi a lokacin da yake ƙoƙarin tabbatar da tsaron yankin. A cewarsa, motar ‘yansandan da ke sintiri ta ofishin ‘yansanda na Garaha ita ma ta ƙone yayin da wani abun  fashewa ya fashe acikin motar amma babu wani mutum da ya rasa ransa. Shugaban ya ce, tsoron bama-baman da maharan ke amfani da su ya sanya zuwa wuraren da aka kai hare-haren ke da matukar wuya. Wa’aganda ya buƙaci a tura sojoji yankin da kuma tallafa wa waɗanda harin ya rutsa da su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar ‘Yansanda Ta Tuhumi Jami’anta Da ‘Yan Kasar Sin Ke Raba Wa Kudi A Wani Bidiyo Da Ke Yawo
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Za A Gudanar Da Zagaye Na Biyu Na Tattaunawar Iran Da Amurka A Birnin Roma Ne
  • WAEC Ta Kwace Lasisin Makarantu 574 Sakamakon Satar Amsa
  • An Kashe Mutane Fiye Da 300 A Wani Kazamin Fada A Yankin Darfur Da Ke Yammacin Kasar Sudan
  • Zargin Ganduje: Za mu sanar da lokacin yanke hukunci —Kotu
  • Hisbah ta kama matashi yana ‘baɗala’ da Akuya a Kano
  • An Kashe Mutane 7 A Yayin Da ‘Yan Ta’adda Suka Ƙaddamar Da Wani Sabon Hari A Adamawa
  • Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas
  • Matashi ya kai kansa ofishin ’yan sanda
  • Kotu ta yanke wa tsohon Shugaban Peru ɗaurin shekaru 15 kan laifin rashawa