China: Kokarin Amurka Ta Haddasa Sabani Tsakanin Moscow Da Beijin Ba Zai Yi Nasar Ba
Published: 27th, February 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen China Lin Jian ne ya jaddada cewa, alakar da take a tsakanin Rasha da China ba ta tasirantuwa da shiga tsakanin wani bangare na uku, sannan kuma ya ce, kokarin da Amurka take yi na haddasa sabani a tsakanin kasashen biyu ba zai yi nasara ba.
A wani taron manema labaru da kakakin ma’aikatar harkokin wajen na China ya gabatar, ya bayar da jawabi akan tambayar da aka yi masa akan maganar da ta fito daga bakin ministan harkokin wajen Amurka Marco Robio cewa; Rasha ta dogara ne China, kuma kasashen biyu za su iya hada kai su yi fada da Amurka.
Li Jian ya kuma ce; Ba tare da la’akari da sauye-sauyen da za su bijiro a fagen siyasar duniya ba, alakar kasashen China da Rasha za ta ci gaba da bunkasa sannu a hankali,don haka kokarin Amruka na haddasa sabani a tsakaninsu ba shi da ma’ana.
A baya kadan shugaban kasar china Xi Jin Ping ya tattauna ta wayar tarho da shugaban kasar Rasha Vladmir Puitn inda ya bayyana masa cewa, alakar kasashen biyu ba za ta tasirantu ba daga tsoma bakin bangare na kuku.
Ita kuwa fadar mulkin Rasha “Kremlin” ta sanar da cewa, alaka a tsakanin Rasha da China da siyasarsu ta waje suna taimakawa wajen samar da zaman lafiya a duniya, kuma ba a gina alakar tasu domin fada da wani bangare ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Da Laberiya Sun Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Ta Fuskar Tattalin Arziki Da Fasaha
Jakadan kasar Sin a kasar Laberiya Yin Chengwu da ministar harkokin wajen kasar Laberiya Sara Nyanti, sun rattaba hannu kan wata yarjejeniyar hadin gwiwa ta fuskar tattalin arziki da fasaha, a madadin gwamnatocin kasashensu, jiya Juma’a a Monrovia, babban birnin kasar Laberiya.
Minista Nyanti ta godewa gwamnatin kasar Sin bisa gagarumin goyon bayan da take bai wa kasar Laberiya, ta kuma ce yarjejeniyar hadin gwiwa ta fuskar tattalin arziki da fasaha da bangarorin biyu suka rattabawa hannu, za ta taimaka wa kasar Laberiya wajen cimma muradin raya kasa na ARREST. Ta ce Laberiya na son yin amfani da wannan dama wajen karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu a fannonin raya kasa, da tattalin arziki, da cinikayya, gami da zuba jari.
A nasa bangare, Ambasada Yin Chengwu ya ce, rattaba hannu kan yarjejeniyar ya nuna cewa, gwamnatin kasar Sin tana kokarin aiwatar da alkawurran da aka dauka a gun taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka yi a birnin Beijing a shekarar 2024, da kuma gudanar da da manyan tsare-tsaren da shugabannin kasashen Sin da Laberiya suka tabbatar. Ya ce kasar Sin tana son aiwatar da yarjejeniyar tare da kasar Laberiya, da kuma sa kaimi ga bunkasuwar hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp