Bankin Raya Afirka ( AFDB) Ya Bayyana Kasashen Da Tattalin Arzikinsu Yake Bunkasa Da Sauri A Cikin Nahiyar
Published: 27th, February 2025 GMT
Bankin Raya Afirka ya sanar da wasu kasashe 10 da ya ce, su ne tattalin arzikinsu yake bunkasa da sauri a cikin nahiyar, tare da yin hashashen cewa gabashin Afirka zai zama sama da sauran yankunan nahiyar a cigaba.
Ana hasashen cewa a cikin rabin kasashen nahiyar za a sami habakar jumillar kudaden shiga ( GDP) daga 4.
A cikin yankin yammacin Afirka kuwa, an tsinkayo cewa tattalin arzikinsu zai tashi daga 4.1% a 2024,zuwa 4.6% a 2025, kuma kasashe irin su Togo, Benin, Cote De Voire, da Gambiya za su sami bunkasa mai karfi.
A Arewacin Afirka kuwa jumillar kudaden shiga ( GDP) zai tashi daga 2.7% a 2024, zuwa 4.2 a 2026.
Kasar Sudan Ta Kudu ce ake hashshen cewa za ta zama zakara a fadin nahiyar ta Afirka wajen bunkasar jumillar kudaden shiga da kaso 34.4%,saboda sake dawowar hako man fetur da kuma fitar da shi zuwa kasuwannin duniya.
Ita kuma Senegal tattalin arzikin nata zai bunkasa ne da kaso 8.9% saboda man fetur, iskar Gas, muhimman cibiyoyi da kuma noma da kiwo.
Kasashen jamhuriyar Nijar, Djibouti, Togo Habasha da Benin da Coye De Voire za su samun bunkasa da kaso 6.3.6.9.% saboda zuba hannun jari a cibiyoyi masu muhimmani da gina su.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Miliyoyin ‘Yahudawa Sun Gudu Neman Mafaka Saboda Makamin Mai Linzami Daga Yemen
Jiniyar gargadi ta kada a cikin sassa masu yawa na Falasdinu dake karkashin mamaya bayan harbo makami mai linzami da mutanen Yemen su ka yi.
Kafafen watsa labarun HKI sun ce, jiniyar gargadin ta kada a cikin garuruwa 255 a HKI daga cikin har da birnin Kudus.
Jaridar “Yediot Ahronot” ta buga labarin dake cewa, wasu barguzan makami mai linzamin sun fada a unguwar “Mifo Hurun”.
Har ila yau harba makami mai linzamin daga Yemen ya sa an dakatar da zirga-zirgar jirage a filin saukar jiragen sama na “Ben Gorion”.
Jaridar “Yesrael Home” ta ce miliyoyin mutane ne su ka shiga dakunan boya saboda kaucewa makami mai linzamin da aka harbo daga Yemen.
A jiya Laraba Sayyid Abdulmalik al-Husi, jagoran kungiyar Ansarullah ya yi alkawalin ci gaba da kai wa HKI hare-hare har zuwa lokacin da za a kawo karshen kai wa Gaza hari, da kuma dauke takunkumin hana shigar da kayan agaji zuwa yankin.
Sayyid Abdulmalik Husi ya kuma kara da cewa, al’ummar Yemen za su ci gaba da yin duk abinda ya dace a kowane mataki domin taimaka wa al’ummar Falasdinu, ta hanyar kai wa HKI hari.
Tun a cikin watan Nuwamba na 2023 ne dai al’ummar Yemen su ka fara kai wa HKI hari a matsayin taya Falasdinawa fada, haka nan kuma sun hana duk wani jirgin ruwa mai zuwa HKI wucewa ta tekun “Red Sea”.
A gefe daya, Amurka da Birtaniya suna ci gaba da kai wa Yemen hare-hare a karkashin kare HKI da suke yi.