Iran Za Ta Rubanya Samar Da Wutar Lantarki Ta Makamashin Nukiliya Har Sau Uku Zuwa 2029
Published: 27th, February 2025 GMT
Jamhuriyar musulunci ta Iran tana shirin aiwatar da shirinta na gina sabbin cibiyoyin samar da wutar lantarki ta hanyar fasahar Nukiliya da kuma fadada wadanda take da su a yanzu.
Shugaban hukumar makamashin Nukiliya ta Iran Muhammad Islami ne ya bayyana hakan, yana mai kara da cewa:
“ Za mu kara yawan wutar lantarkin da muke samarwa da megawati 2000 a kowace sa’a daya daga nan zuwa karshen zangon na bakwai na tsare-tsaren ci gaba da ake yi a kowace shekara 5.
Salami ya ce za a kara megawati 1,000 a cikin kowace sa’a da hakan zai mayar da abinda ake samarwa zuwa megawati 3,000 a cikin kowace sa’a.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Miliyoyin ‘Yahudawa Sun Gudu Neman Mafaka Saboda Makamin Mai Linzami Daga Yemen
Jiniyar gargadi ta kada a cikin sassa masu yawa na Falasdinu dake karkashin mamaya bayan harbo makami mai linzami da mutanen Yemen su ka yi.
Kafafen watsa labarun HKI sun ce, jiniyar gargadin ta kada a cikin garuruwa 255 a HKI daga cikin har da birnin Kudus.
Jaridar “Yediot Ahronot” ta buga labarin dake cewa, wasu barguzan makami mai linzamin sun fada a unguwar “Mifo Hurun”.
Har ila yau harba makami mai linzamin daga Yemen ya sa an dakatar da zirga-zirgar jirage a filin saukar jiragen sama na “Ben Gorion”.
Jaridar “Yesrael Home” ta ce miliyoyin mutane ne su ka shiga dakunan boya saboda kaucewa makami mai linzamin da aka harbo daga Yemen.
A jiya Laraba Sayyid Abdulmalik al-Husi, jagoran kungiyar Ansarullah ya yi alkawalin ci gaba da kai wa HKI hare-hare har zuwa lokacin da za a kawo karshen kai wa Gaza hari, da kuma dauke takunkumin hana shigar da kayan agaji zuwa yankin.
Sayyid Abdulmalik Husi ya kuma kara da cewa, al’ummar Yemen za su ci gaba da yin duk abinda ya dace a kowane mataki domin taimaka wa al’ummar Falasdinu, ta hanyar kai wa HKI hari.
Tun a cikin watan Nuwamba na 2023 ne dai al’ummar Yemen su ka fara kai wa HKI hari a matsayin taya Falasdinawa fada, haka nan kuma sun hana duk wani jirgin ruwa mai zuwa HKI wucewa ta tekun “Red Sea”.
A gefe daya, Amurka da Birtaniya suna ci gaba da kai wa Yemen hare-hare a karkashin kare HKI da suke yi.