Malaman Jami’ar Sakkwato sun tsunduma yajin aiki
Published: 27th, February 2025 GMT
Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato, sun fara yajin aiki a karon farko tun bayan kafuwar jami’ar sama da shekaru 12 da suka gabata.
A wata sanarwa da shugabansu, Saidu Isah Abubakar, tare da Sakataren Jami’ar, Hassan Aliyu, suka fitar, sun bayyana cewa an yanke shawarar shiga yajin aikin ne a ranar Laraba.
“Dukkanin harkokin karatu, karantarwa, jarabawa, duba ɗalibai da makin jarabawa sun tsaya har sai an cimma matsaya,” in ji sanarwar.
Malaman sun ce sun ɗauki wannan mataki ne domin tilasta wa gwamnatin jihar, biyan buƙatun da suka jima suna gabatarwa.
Sanarwar, ta ce ba su gamsu da yadda gwamnati da majalisar gudanarwar Jami’ar ke tafiyar da al’amuran da suka shafi ci gaban Jami’ar ba.
Saboda haka, a taron da suka gudanar, mambobin ƙungiyar sun amince da fara yajin aiki daga ranar 26 ga watan Fabrairu, 2025.
Ƙungiyar ta ce ta kafa kwamitin da zai tabbatar da an bi umarnin yajin aikin a Jami’ar.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Biya Sama Da Naira Miliyan 730 Ga Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya
Hukumar fansho ta jihar Jigawa da kananan hukumomin jihar ta fara biyan sama da naira miliyan 733 ga ma’aikata sama da 280 da suka yi ritaya da kuma ‘yan uwan ma’aikatan da suka rasu.
Shugaban hukumar Dakta Bilyaminu Shitu Aminu ne ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi ga wadanda abin ya shafa a ofishin fansho da ke Dutse babban birnin jihar.
Ya bayyana cewa kudaden sun hada da na barin aiki, da na ma’aikatan da suka mutu.
A cewarsa, ma’aikatan 281 sun hada da na jiha, da kananan hukumomi da na hukumar ilimi, wadanda suka yi ritaya na son rai ko kuma sun kai shekarun ritaya ko kuma wadanda suka mutu suna aiki.
Dakta Bilyaminu Shitu ya ci gaba da bayanin cewa za a biya ma’aikata 208 da suka yi ritaya daga aiki sama da naira 542, yayin da za a biya sama da Naira miliyan 144 ga ‘yan uwan wadanda suka mutu a bakin aiki su 47.
A cewarsa, rukunin karshe su ne ma’aikata 26 da suka yi ritaya daga aiki kuma suka fara karbar fansho duk wata amma sun mutu kafin su kai wa’adin mafi karancin shekaru biyar bayan sun yi ritaya.
Shugaban hukumar ya bayyana cewa jihar Jigawa na daya daga cikin jihohin da ke da kyakkyawan tsarin fensho mafi inganci a kasar nan, duba da yadda ta ke kokarin biyan wadanda suka yi ritaya ba tare da wata matsala ba kuma akan lokaci.
Ya ce wannan gagarumin ci gaba ya nuna irin yadda gwamnatin jihar ta himmatu wajen kyautata rayuwar ‘yan fanshonta da kuma muhimmancin tabbatar da biyan hakkokin wadanda suka yi wa jihar hidima.
Shugaban ‘yan fanshon ya ce, hukumar ta jajirce wajen tabbatar da biyan kudaden fansho cikin lokaci da inganci kuma tana sa ran za ta ci gaba da yin sabbin abubuwa da nufin inganta jin dadin ‘yan fanshonta.
Biyan kudaden da aka gudanar a hedikwatar hukumar fansho ta jihar Jigawa dake Dutse, wani bangare ne na kokarin karrama kwazon ma’aikatan gwamnati da suka sadaukar da kai wajen yi wa jihar hidima.
Shugaban hukumar ya kuma yabawa Gwamna Malam Umar Namadi bisa irin goyon bayan da yake bai wa hukumar.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, wadanda aka biya hakkokin nasu, sun nuna jin dadinsu da yadda aka biya su akan lokaci.
Sun yi nuni da cewa, biyansu kudaden zai ba su damar sauke nauyin da ya rataya a wuyansu da kuma inganta rayuwarsu a lokacin ritaya.
Usman Muhammad Zaria