MDD Ta Yi Gargadi Akan Tsanantar Yunwa A Kasar Sudan
Published: 27th, February 2025 GMT
A jiya Laraba ne dai Hukumar da take kula da harkokin jin kai dake karkashin MDD ( OCHA) ta bayyana cewa; Kusan shekaru biyu na yakin da ake yi a Sudan ya kara tsananta, kuma a halin yanzu yunwa wani abu ne da ya zama dahir ana ganinta a kasa a Sudan.
Babbar daraktan gudanar da ayyukan hukumar agajin ta MDD Edem Wosornu ta fadawa kwamitin tsaron MDD cewa; Da akwai mutane miliyan 12 da aka tarwasta daga gidajensu, daga cikinsu da akwai wasu miliyan 3.
Haka nan kuma ta kara da cewa; Tsarin kiwon lafiya na kasar ya durkushe baki daya, da akwai miliyoyin kananan yara da su ka daina karatu, wasu kuma an ci zarafinsu.”
Bugu da kari, saboda fadan da ake ci gaba da yi, an dakatar da kai kayan agaji zuwa sansanin ‘yan hijira mafi girma na Zamzam, alhali suna da bukatuwa da agajin.
A ranar Litinin da ta gabata ne dai kungiyar likitoci ba tare da iyaka ba ( Médecins Sans Frontières ) ta nuna rashin jin dadinta da yadda rashin tsaro ya tilasata ta dakata da ayyukanta a sansanin Zamzam.
Jakadan Sudan A MDD Al-Harith Idriss ya ce, kasarsa a shirye take ta samar da yanayin da zai bayar da damar ci gaba da gudanar da ayyukan agaji a kasar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Abubuwan Da Za Su Iya Kawo Cikas Ga Bukukuwan karamar Sallah
Tsadar rayuwa tun daga wancan lokacin ne bayan cire tallafin mai,da kwana daya kawai zuwa biyu sai rayuwar wasu dole ta fara sauyawa,kaya ko kayayyakin da ake saya a farashi na kashi 75 zuwa 100 sai abin ya koma farashin wasu har sai da,ya kai kashi 200 zuwa kashi 300 kai wani abin ma, har ya zarce haka,kuma kamar yadda Hausawa suka ce dole ce kanwar na ki ta sa hakan ta kasance,wannan kuma haka ne. Dole ce tasa haka saboda har an kai ga ganin abinda ya cirewa Buzu nadi wato wahala ke nan.Kuma dole ne cin kasuwa da makiyi wasu abubuwan abin ba,a iya cewa komai sai dai ayi gum da Baki kawai.
Matsalar tsaro
Ko shakka babu lamarin tavarvarewar tsaro ba karamin koma baya ya kawo ba na lamarin zamantakewa tsakanin al’umma abu tun daga wannan unguwa zuwa waccan har,ta kai ga daga wannan babban gari ma zuwa wancan har ta kai ga daga wannan Jiha zuwa waccan.Irin halin da al’umma suka tsinci kansu ke nan lamarin da ya kan yi tafiyar Kura yadda take gaba sai ta koma baya. Arewa ta sassa daban- daban tana fama da matsalar data shafi tsaro tunda kuwa ana yin garkuwa lokaci,anan matafiya wasu Jihohi na sashen Arewa maso yamma kamar Kaduna, Katsina,Zamfara,Sakkwato,da kuma Kebbi,masu ta shi daga Abuja zuwa gida wasu suna kan hanyar tasu ake tsaida su a kwashi mutane kamar Dabbobi ayi cikin daji dasu,kai har ma,ta kai ga mutane ko,a gidajensu suke basu tsira ba ana iya zuwa kowane lokaci ayi awon gaba dasu sai kuma yadda Allah yayi.Yayin da wasu suna dawowa wasu kuwa sun tafi ke nen sai dai aji labarin an kashe su,wasu ko ma an kai kudin fansar ba,za’a sake su ba.Irin hakan ce ta sa wasu yanzu basu zuwa gida Sallah saboda tsoron aukuwar irin hakan,maimakon hakan sai su yi hakuri su rungumi kaddara ta yin rayuwa kamar irin cikin halin,da suka samu kansu.
Tafiya zuwa yawon Sallah daga wannan unguwa zuwa waccan ko daga wannan gari zuwa wancan,halin da ake ciki yanzu hakan bata yiyuwa ba domin komai ba sai saboda tsoron irin abinda ka iya faruwa gare su,maganar gaskiya yanzu lamarin tsaro ya sa mutane da yawa sun,shiga cikin halin tsoro saboda komai yana iya faruwa a lokacin da ba ayi tsammanin hakan ba.Ba ance babu tsaron bane gaba daya amma su wadannan masu tayar,da zaune tsaye ko ina suna iya zuwa saboda ai suna da wadanda suke basu halin da ake ciki da su kan samu na su kason idan an yi sa’ar dauka da kuma garkuwa da mutane aka kuma biya kudin fansar.
Al’umma da dama basa garuruwan su na asali
Mutane da dama yanzu wasu ma ba Jihar su ta asali suke ba,wasu suna wata Jiha,kai akwai ‘yan Nijeriyar da har yanzu suna kasashen Nijar ko kuma Kamaru,idan ma sun yi sa’ar suna Jihar tasu ne,to su kan kasance ne a wani sansanin ‘yan gudun hijira ne wato wuraren da aka tsugunnar dasu,sanin kowa ne,babu yadda rayuwa za ta yi daidai ga wasu a,irin wadancan wuraren saboda can ma din da akwai nau’oin matsalolin da suke fuskanta a can.Ana iya tunawa shifa sansanin ‘yan gudun hijira wuri ne da aka ware na musamman wanda ake taimakawa nau’oin mutanen da suka fuskanci matsala babu yadda za su iya yi wajen tafiyar da rayuwarsu.Daga karshe sanin kowa ne duk wanda bai garin shi na asali rayuwa Lami yake yin ta domin a matukar takure yake.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp