HausaTv:
2025-04-19@22:59:00 GMT

MDD Ta Yi Gargadi Akan Tsanantar Yunwa A Kasar Sudan

Published: 27th, February 2025 GMT

A jiya Laraba ne dai Hukumar da take kula da harkokin jin kai dake karkashin MDD  ( OCHA) ta bayyana cewa; Kusan shekaru biyu na yakin da ake yi a Sudan ya kara tsananta, kuma a halin yanzu yunwa wani abu ne da ya zama dahir ana ganinta a kasa a Sudan.

Babbar daraktan  gudanar da ayyukan hukumar agajin ta MDD Edem Wosornu ta fadawa kwamitin tsaron MDD cewa; Da akwai mutane miliyan 12 da aka tarwasta daga gidajensu, daga cikinsu da akwai wasu miliyan 3.

4 da su ka tsallaka iyaka. Haka nan kuma fiye da rabin mutanen kasar Miliyan 24.6 suna fama da matsananciyar yunwa.”

Haka nan kuma ta kara da cewa; Tsarin kiwon lafiya na kasar ya durkushe baki daya, da akwai miliyoyin kananan yara da su ka daina karatu, wasu kuma an ci zarafinsu.”

Bugu da kari, saboda fadan da ake ci gaba da yi, an dakatar da kai kayan agaji zuwa sansanin ‘yan hijira mafi girma na Zamzam, alhali suna da bukatuwa da agajin.

A ranar Litinin da ta gabata ne dai kungiyar likitoci ba tare da iyaka ba        ( Médecins Sans Frontières )  ta nuna rashin jin dadinta da yadda rashin tsaro ya tilasata ta dakata da ayyukanta a sansanin Zamzam.

Jakadan Sudan A MDD Al-Harith Idriss ya ce, kasarsa a shirye take ta samar da yanayin da zai bayar da damar ci gaba da gudanar da ayyukan agaji a kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Makasudin Rubuta Sakon Jagora Ga Shugaban Kasar Rasha

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Sakon jagora ga shugaban kasar Rasha yana da alaka da ci gaban kasa da kasa da na yanki

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana hakan ne a yau Alhamis a birnin Moscow na kasar Rasha cewa: Abu ne da ya dace a rubuta sakon da Jagoran juyin juya halin Musulunci ya aikewa shugaban kasar Rasha dangane da ci gaban kasa da kasa da na yanki da kuma batutuwan da suka shafi kasashen biyu.

Araqchi ya bayyana hakan ne a lokacin da ya isa filin tashi da saukar jiragen sama na Vnukovo da ke birnin Moscow a yau, yayin da yake amsa tambayar da wakilin IRNA ya yi masa kan abubuwan da ke cikin sakon jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei zuwa ga shugaban kasar Rasha Vladimir Putin.

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya kara da cewa: Ziyarar tasa tana da manufofi daban-daban, yana mai bayanin cewa, tun da farko an shirya ziyarar ne domin isar da rubutaccen sako daga Jagoran juyin juya halin Musulunci ga shugaban kasar Rasha, kuma ta zo daidai da abubuwan da suka faru a baya-bayan nan da kuma tattaunawa ta kai tsaye.

Ya kara da cewa, tun a baya, har ya zuwa yanzu, a ko da yaushe Iran tana gudanar da shawarwari na kut-da-kut da abokanta na kasar Rasha kan batun makamashin nukiliya, yana mai cewa, suna kuma tattaunawa da Rasha da China, kuma a yanzu da aka samu damar da ta dace, za a iya yin shawarwari tare da jami’an Rasha.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Muna Ganin Kashe-kashe Ta Ko’ina – ‘Yan Gudun Hijirar Sudan
  • Sojojin Sudan Sun Kashe ‘Yan Tawayen Kasar Ciki Har Da Manyan Kwamandojinsu A Birnin El Fasher
  • Amurka Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadancinta Kimani 30 A Duniya
  • Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Ta Sake Aiwatar Da Kisan Kiyashi A Sansanin Falasdinawa Na Jabaliya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Makasudin Rubuta Sakon Jagora Ga Shugaban Kasar Rasha
  • An Kashe Mutane Fiye Da 300 A Wani Kazamin Fada A Yankin Darfur Da Ke Yammacin Kasar Sudan
  • Kasar Pakistan Ta Kara Jaddada Dokar Rashin Amincewa Da HKI A Matsayi Kasa
  • MDD Ta Nuna Damuwarta Akan Kokarin Sake Raba Kasar Sudan Gida Biyu
  • Iran Ta Damu Akan Mummunan Yanayin Da Mutanen Al-Fasha Na Sudan Suke Ciki
  • WTO Ta Yi Gargadi Akan Karin Kudin Fito Na Amurka