Kwanan baya, kwamitin kula da aikin lantarki na duniya (IEC) ya gabatar da ka’idar sarrafa mutum-mutumin inji mai kula da tsoffi. Ka’idar da kasar Sin ta ba da jagorancin tsarawa, ta tabbatar da yadda za a tsara da sarrafa mutum-mutumin injuna masu kula da tsoffi bisa halayen da tsoffi suke ciki, ta kuma tabbatar da yadda za a gudanar da bincike kan mutum-mutumin inji, yayin ba da izini gare su.

Lamarin da ya ba da tabbaci ga bunkasuwar aikin sarrafa mutum-mutumin injuna masu kula da tsoffi yadda ya kamata.

Bayanin ya nuna cewa, an tsara ka’idar bisa bukatun tsoffi a fannonin samun kulawa cikin harkokin yau da kullum, da kiwon lafiya da dai sauransu. Haka kuma, ana fatan tsara mutum-mutumin inji bisa mabambanta bukatu, ban da ingancinsu, da tsimin makamashi, ana kuma fatan za su iya sa ido kan lafiyar jiki, da gudanar da harkokin gaggawa yadda ya kamata, tare da tuntubar iyalan tsoffi da masu ba da jinya cikin lokaci da dai sauransu. (Mai Fassara: Maryam Yang)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Za Ta Kara Matsa Kaimi Ga Raya Sha’anin Mata Na Duniya

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian ya bayyana a yau cewa, bana shekara ce ta cika shekaru 30 da gudanar da taron harkokin mata na duniya na Beijing. Kuma kasar Sin za ta ci gaba da amfani da damar da aka samu ta cika shekaru 30 da zartas da sanarwar Beijing da shirin ayyuka, da yin kokari tare da kasahen duniya wajen sa kaimi ga raya sha’anin mata na duniya.

Lin Jian ya bayyana cewa, a ranar 24 ga watan Fabrairu, an gudanar da taron tattaunawa kan murnar cika shekaru 30 da zartas da sanarwar Beijing da shirin ayyuka bisa bukatun Sin da wasu kasashen da abin ya shafa, a yayin da majalisar kare hakkin dan Adam ta MDD ta gudanar da taronta karo na 58, inda shugabannin hukumomin MDD mata suka halarci taron tare da gabatar da jawabi.

Lin Jian ya ce, a matsayin ‘yar sama jannati ta farko ta kasar Sin wadda ta shiga sararin samaniya, Liu Yang ta yi jawabi ta kafar bidiyo cewa, tunanin zaman daidaito na sha’anin binciken sararin samaniya na kasar Sin ya nuna cewa, kasar Sin tana kokarin raya sha’anin mata, wato tabbatar da yanayin yin takara cikin adalci ta bisa kyakkyawan tsari, kuma wannan ne aikin da aka gudanar bisa tunanin sanarwar Beijing. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • CMG Ya Kaddamar Da Gasar Basirar Mutum-mutumin Inji Ta Duniya 
  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Tabbatar Da Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya
  • Sin Za Ta Kara Matsa Kaimi Ga Raya Sha’anin Mata Na Duniya
  • Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno
  • An Gudanar Da Taron Dandalin Ciniki Tsakanin Sin Da Habasha A Addis Ababa
  • Mutum 10 sun mutu a hanyar Damaturu zuwa Maiduguri
  • 40% na matan Kano sun fuskaci cin zarafi a gida —Shugaban Majalisa
  • Mutum 7,000 Suka Mutu A Rikicin Gabashin Kwango Tun Daga Watan Janairu
  • Ya Kamata Trump Ya Yi Koyi Da Nixon