Boko Haram: An lalata gidaje da makarantu a ƙauyukan Adamawa
Published: 27th, February 2025 GMT
Wasu gungun ‘yan Boko Haram ɗauke da muggan makamai sun kai farmaki cikin dare a garin Kwapre da ƙauyukan da ke gundumar New Yadul a ƙaramar hukumar Hong a Jihar Adamawa.
Harin wanda ya fara daga misalin ƙarfe 7:30 na yammacin ranar Talata, 25 ga watan Fabrairu, kuma ya ɓarnata dukiyoyi a tsakiyar daren.
Al’ummar yankin sun ce, an ƙona wuraren ibada da makarantu da gidaje da wuraren kasuwanci, sannan an wawushe dukiyoyi na miliyoyin Naira.
Mista Joel Kulaha, Hakimin garin Kwapre da Abalis Jawaja, kuma dagacin ƙauyen, ya ce maharan sun farwa al’ummar garin, inda suka ƙona gine-gine tare da kwashe kayayyaki masu daraja.
Sun ce, an yi sa’a ba a rasa rayuka a harin ba, domin mazauna yankin sun yi gargaɗin ƙaruwar barazanar harin, sun tsere daga gidajensu kafin maharan su iso.
“Mun tsere da rayukanmu, amma duk abin da muka mallaka ya tafi,” kamar yadda Kulaha ya koka, yana kwatanta harin da aka kai.
An samu rahoton cewa dakarun sojin da ke kusa da Garaha sun mayar da martani kan harin da sanyin safiya, inda suka fatattaki maharan.
Sai dai mazauna yankin sun ce matakin sojan ya makara ne domin daƙile ɓarnar da ta ɓarke ƙauyukan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Adamawa Boko Haram Kwapre Hong
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamitin Gudanar da Kasuwa Maras Shinge Ta Maigatari Sun Ziyarci Fadar Gumel
Masarautar Gumel ta ce za ta bayar da dukkan goyon baya da hadin kai da ake bukata domin ci gaban yankin kasuwancin da ba shida shinge na Maigatari a jihar Jigawa.
Mai Martaba Sarkin Gumel Alhaji Ahmad Mohammad Sani ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin mambobin kwamitin Jiha mai kula da shiyyar fitar da kaya ko kasuwanci maras shinge na Maigatari a fadar sa.
Ya ce, nan ba da dadewa ba majalisar masarautar za ta shirya taro da hakiman Gundumomi da Unguwanni da Kauyuka domin fadakar da al’ummarsu kan gudunmawar da suke bukata domin samun nasarar wannan yankin.
Sarkin wanda ya samu wakilcin Dallatun Gumel, Alhaji Musa Ayuba ya ce aikin noman rani da asibitin kashi da cibiyar dialysis da gwamnatin Malam Umar Namadi ta kafa a Gumel ayyuka ne da ke yin tasiri kai tsaye ga rayuwar al’ummar yankin.
Tun da farko shugaban kwamitin kula da shiyyar fitar da kaya da babu haraji ko shinge na jiha kuma kwamishinan kasafin kudi da kididdiga Alhaji Babangida Umar Gantsa ya ce sun je fadar sarkin ne domin sanar da shi irin nasarorin da aka samu tare da neman hadin kan sa da addu’o’i na uba.
Gantsa, ya kara da cewa gwamnati ta kashe makudan kudade wajen samun Amincewa da Lasisi domin sanya Maigatari fa matsayin wata kasuwa ko yanki da za a yi cinikayya maras shinge ko haraji don bunkasar Jihar Jigawa da kasa baki daya.
Shima da yake nasa jawabin Hakimin Gumel Arewa, Alhaji Sani Abdullahi Babandi ya yi kira ga ‘yan kwamitin da su tuntubi hukumomin da abin ya shafa don gyara hanyar gwamnatin tarayya da ta hada Gumel zuwa Maigatari domin samun damar shiga yankin cikin kwanciyar hankali.
USMAN MZ