Aminiya:
2025-04-19@06:15:08 GMT

Zargin Almundahana: Kotu ta ba da belin Farfesa Usman

Published: 27th, February 2025 GMT

Wata Babbar Kotu a Abuja, ta bayar da belin tsohon shugaban Hukumar Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIS), Farfesa Usman Yusuf, wanda ake tuhuma da almundahana.

A ranar Alhamis, Mai Shari’a Chinyere Nwecheonwu, ta bayar da umarnin sakin Farfesa Usman daga gidan gyaran hali na Kuje bayan an cika sharuɗan belinsa.

Boko Haram: An lalata gidaje da makarantu a ƙauyukan Adamawa Malaman Jami’ar Sakkwato sun tsunduma yajin aiki

Hukumar EFCC ce, ta gurfanar da shi kan tuhume-tuhume guda biyar da suka haɗa da zargin karkatar da kuɗaɗe.

Ana zargin ya amince wajen sayen motoci a kan Naira miliyan 49.2 maimakon Naira miliyan 30 da aka ware a matsayinsa na shugaban NHIS a 2016.

EFCC, ta kuma ce Farfesa Usman ya bai wa wani kamfani mai suna Lubekh Nigeria Limited kwangilar yaɗa labarai da hulɗa da jama’a ta Naira miliyan 17.5 ta hannun ɗan uwansa, Khalifa Hassan Yusuf.

Duk da haka, Farfesa Yusuf ya musanta dukkanin zarge-zargen da ake yi masa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farfesa Usman

এছাড়াও পড়ুন:

BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano

Cibiyar Nazarin Dimokuradiyya ta Aminu Kano a Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta shirya taron shekara-shekara karo na 23 don tunawa da cika shekaru 42 da rasuwar Malam Aminu Kano.

 

 

A nasa jawabin, Shugaban jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya jaddada muhimmancin taron shekara-shekara wajen kiyaye manufofin da Malam Aminu Kano ya tsaya a kai.

 

Farfesa Haruna Musa wanda mataimakin shugaban jami’ar kula da harkokin ilimi ya wakilta, ya bayyana cewa jerin laccoci an yi niyya ne don ba da damar fahimtar juna dangane da yanayin tarihi.

 

“A ci gaba da kokarin da jami’ar mu ke yi na karfafa al’adun dimokuradiyyar Najeriya, muna gayyatar manyan mutane duk shekara don gabatar da laccoci a gidan Mambayya kan batutuwan da suka shafi kasa baki daya.

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabiru Yusuf, ya bayyana Malam Aminu Kano a matsayin wani hamshakin mai neman sauyi na Afirka, kuma dan gwagwarmayar siyasa mai jajircewa, wanda rayuwarsa ke ci gaba da zaburar da al’umma.

 

 

Wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya jaddada cewa taken taron ya dace saboda halin da kasar nan ke ciki.

 

A nasa jawabin, Farfesa Kabiru Isa Dandago ya gabatar da kasida mai taken “Siyasar Gyaran Haraji a Najeriya: Tsammani da Gaskiya.

 

Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa taron tunawa da marigayin ya hada masana, masana siyasa, da shugabannin kungiyoyin farar hula, inda suka yi bita a kan rayuwar marigayi dan kishin kasa, malami, dan juyin juya hali.

 

KHADIJAH ALIYU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • China Ta Musanta Zargin Ukraine Na Tallafawa Rasha Da Makamai
  • BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Makasudin Rubuta Sakon Jagora Ga Shugaban Kasar Rasha
  • Hukumar Alhazai ta Jigawa Ta Shirya Bitar Ga Malaman Bita na Kananan Hukumomi 27
  • Hukumar EFCC Ta Kama Mutane 40 da Ake Zargi da Damfarar Intanet
  • Zargin Ganduje: Za mu sanar da lokacin yanke hukunci —Kotu
  • Kamfanonin Lantarki Na Shirin Shiga Yajin Aiki Kan Bashin Naira Tiriliyan 4
  • Matashin Da Ya Ƙware Wajen Kashe Mutane Da Ƙwace Ya Miƙa Kansa Ga ‘Yansanda A Kano
  • Kotu ta yanke wa tsohon Shugaban Peru ɗaurin shekaru 15 kan laifin rashawa
  • Kotu ta yanke wa tsohon Shugaban Peru ɗaurin shekaru 15