Leadership News Hausa:
2025-03-30@09:56:37 GMT

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Janye Bincike Kan Shigo Da Jan Karfe

Published: 27th, February 2025 GMT

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Janye Bincike Kan Shigo Da Jan Karfe

Ma’aikatar harkokin cinikayya ta kasar Sin ta bukaci Amurka da ta gaggauta janye binciken sashe na 232 kan shigo da jan karfe kasarta, inda ta bayyana cewa, zargin da ake yi na cewa kasar Sin na amfani da tallafin gwamnati da karfin samar da hajoji fiye da kima don gurgunta abokan takara kwata-kwata ba ya da tushe.

Kakakin ma’aikatar He Yadong ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a lokacin da yake amsa tambaya kan matakin da Amurka ta dauka na kaddamar da binciken sashe na 232 kan jan karfe da aka shigar da su kasar daga kasashen waje.

Ya kara da cewa, binciken na Amurka wani aiki ne na kashin kai da kariyar cinikayya wanda ta yi bisa fakewa da “tsaron kasa”, kuma matakin zai kara yin illa ga tsarin cinikayyar bangarori daban daban da kuma kawo cikas ga daidaiton tsarin samarwa, da rarraba hajoji tsakanin sassan kasa da kasa.

Kakakin ya ce, idan Amurka ta nace kan sanya karin haraji da sauran matakan takaitawa, Sin za ta dauki dukkan matakan da suka dace don kiyaye hakkoki da moriyarta. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Bada Amsa Ga Wasikar Shugaban Kasar Amurka Ta Gayyatar Kasar Zuwa Tattaunawa Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa gwamnatin kasar ta Mayarwa Shugaban kasar Amurka Donal Trump amsar wasikarsa ga kasar danagne da shirinta na makashain Nulkiya ta hanyar kasar Omman.

Aragchi ya bayyana haka a jiya Alhamis a lokacinda yake hira da kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran.

Ya kuma kara da cewa a cikin wasikar dai gwamnatin JMI bayyanawa shugaban kan cewa tana ganin bazata iya shiga tattaunawa gaba da gaba da Jami’an gwamnatin kasar Amurka dangane da shirinta na makamashin Nukliya ba, saboda halayen gwamnatocin Amurka a baya dangane da shirin.

Daga ciki Iran ta dauke shekaru biyu cutar tana tattauna batun wannan shirin da manya-manyan kasashen duniya daga ciki har da kasar Amurka,  aka cimma yarjeniya a shekara ta 2015, kuma har an fara aiwatar da yarjeniyar ta JCPOA, amma gwamnatin Amurka ta lokacinda wanda shugaba mai ci yake jagoranta ta fice daga cikin yarjeniyar ba tare da wani dalili ba, sannan ta dorawa Iran sabbin takunkuman tattalin arziki mafi muni a tarihin kasar da nufin tilasta mata da sake wata tattaunawa  da ita. Waya ya sani mai yuwa da sake saba alkawalin da aka cimma da ita a wannan karon ma, bayan wancan?. Amma ta kasa samun nasara har ta sauka.

Banda haka a lokacinda wannan gwamnatin ta zo kan karagar shugabancin Amurka ta fara kara dorawa JMI wasu karin takunkuman tattalin arziki kafin ma ta gayyana kasar zuwa tattaunawa.

Wannan ya nuna cewa ba tattaunawa take bukata ba, sai dai tursasawa. Wanda kasar Iran baza ta taba amincewa da haka ba.

Sannan idan Amurka ta na son shiga tattaunawa da Iran kan shirinta na makamashin Nukliya to a halin yanzu ma tana tattaunawa da kasashen turai uku kan shirin nata. Sai ta shigo.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani Jami’in Leken Asirin HKI Ya Bukaci Kasashen Afirka Su Taimaka Su Karmi Falasdinawan Da Za;a Kora Daga Gaza
  • Kwamandan IRGC Ya Gargadi Amurka Dangane Da Hari Kan Kasar A Ranar Qudus Ta Duniya
  • Kungiyar “White Helmets Ta” A Kasar Siriya Ta Rasha Tallafin Da Take Samu Daga USAID
  • Maduro Ya Bayyana Sakataren Harkokin Wajen Amurka Da Cewa Wawa Ne
  • Shugaban CMG Ya Gana Da Ministar Raya Al’adu Ta Rasha
  • Iran: Ta’addancin sojojin Amurka a kan Yemen ‘barazana’ ne ga zaman lafiyar duniya
  • Xi Jinping Ya Gana Da Wakilan Masana’antu Da Cinikayya Na Kasa Da Kasa
  • Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba
  • Iran Ta Bada Amsa Ga Wasikar Shugaban Kasar Amurka Ta Gayyatar Kasar Zuwa Tattaunawa Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya
  • Kasar Sin Na Adawa Da Kara Yawan Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Amurka Ta Takaita Fitar Da Kayayyakinsu