Taron lakca karo na 22 na kasar Sin da aka yi jiya Laraba a birnin Alkahiran Masar, ya hada malamai Sinawa da na kasar da jami’ai sama da 200, inda suka tattauna don gane da zurfafa hadin gwiwar Sin da Afrika, wajen daukaka zamanantar da kasashe masu tasowa.

Cibiyar nazarin dangantakar Sin da Afrika da cibiyar Confucius ta jami’ar Suez Canal ta Masar ne suka karbi bakuncin taron mai taken “Zurfafa hadin gwiwar Sin da Afrika domin jagorantar zamanantar da kasashe masu tasowa.

” Taron ya mayar da hankali ne kan karfafa dangantakar Sin da Masar, da fadada musaya tsakanin masana, da bunkasa tallafin ilimi ga kokarin kasashe masu tasowa na zamanantar da kansu.

Tattaunawar ta kuma jaddada batun kara inganta hadin gwiwar Sin da Afrika yayin da ake fama da sauye-sauye a duniya.

Da yake tsokaci, Hassan Rajab, daraktan cibiyar Confucius ta jami’ar Suez Canal, ya nanata raya al’adun bangarori daban daban a matsayi mai muhimmanci ga dangantakar Sin da Afrika, yana mai alakanta ta da shawarar wayewar kan al’ummar duniya da Sin ta gabatar. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Me Sabon Karfin Samar Da Ci Gaban Ayyukan Gona Zai Kawo Mana?

Akwai makoma mai haske wajen raya sabon karfin samar da ci gaban ayyukan gona, wanda tabbas zai taimaka wa Sin da kasashen Afirka wajen gaggauta zamanantar da ayyukan gona, har ma da zamanantar da kasashensu baki daya.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Me Sabon Karfin Samar Da Ci Gaban Ayyukan Gona Zai Kawo Mana?
  • Shugaban Hafsan Sojan Sama Na Najeriya Ya Zama Shugaban Kungiyar Sojojin Sama Na Afrika
  • Gwamna Sule Ya Hori Masu Ziyarar Ibada Ta Kirista Su Zama Jakadu Na Gari
  • Sin Za Ta Kara Matsa Kaimi Ga Raya Sha’anin Mata Na Duniya
  • Mugunta Fitsarin Fako…
  • Gwamnatin Katsina Ta Ƙaddamar Da Shirin Tallafin Abinci Na Naira Biliyan 4
  • An Gudanar Da Taron Dandalin Ciniki Tsakanin Sin Da Habasha A Addis Ababa
  • IRGC : Jana’izar Nasrallah Wani Sakon ‘yan Gwagwarmaya A Duniya Baki Daya
  • Araghchi : Bai Kamata A Rika Murgude Hakkin Dan Adam Ana Shishigi A Harkokin Cikin Gidan Kasashe Ba