Leadership News Hausa:
2025-02-28@02:39:52 GMT

CMG Ya Kaddamar Da Gasar Basirar Mutum-mutumin Inji Ta Duniya 

Published: 28th, February 2025 GMT

CMG Ya Kaddamar Da Gasar Basirar Mutum-mutumin Inji Ta Duniya 

A ranar 27 ga wata ne babban gidan rediyo da talibijin na kasar Sin na CMG ya kaddamar da gasar basira ta mutum-mutumin inji ta duniya a birnin Beijing.

Babban daraktan CMG Shen Haixiong ya bayyana cewa, masana’antar mutum-mutumin inji ta zama wata muhimmiyar alama ta auna matsayin wata kasa ta fuskar kimiyya da fasahar kere-kere da kuma masana’antar kere-kere na babban mataki.

Kasar Sin ta zama kasa mafi grima a duniya wajen kera mutum-mutumin inji da yin amfani da su. Ta hanyar dogaro da babban dandalin watsa labaru mai karfi, gasar basira ta mutum-mutumin inji ta duniya ta CMG za ta nuna nasarorin da aka samu wajen kera mutum-mutumin inji ta kowane bangare, ta yadda za a hada karfin kimiyya da fasaha da kuma al’adun gargajiya waje guda, ta yadda ainihin kirkire-kirkire da ayyaukan kula da dan Adam za su kyautata tare. Ana sa ran wannan gasa za ta sa kaimi ga ci gaban fasahar mutum-mutumin inji da kuma ba da gudummawa wajen gina kasar Sin mai karfin kimiyya da fasaha da gina al’umma mai makomar bai daya ga bil Adama. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 7,000 Suka Mutu A Rikicin Gabashin Kwango Tun Daga Watan Janairu

Fiye da mutane 7,000 da yawancinsu fararen hula ne aka kashe a yankin gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango tun daga watan Janairu, in ji Firaminista Judith Suminwa Tuluka a ranar Litinin.

Mambobin kungiyar M23 da ke samun goyon bayan kasar Rwanda sun kwace iko da yankunan gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kongo masu arzikin ma’adinai da suka hada da manyan biranen Goma da Bukavu da ke gabashin kasar.

Firayim Minista Judith Suminwa Tuluka ta yi gargadin cewa, halin da ake ciki na tsaro a gabashin DRC ya kai matsayi mai daukar hankali, yayin da take jawabi ga kwamitin kare hakkin bil’adama na Majalisar Dinkin Duniya a Geneva.

Ta ce mutanen da suka mutu sun hada da “fiye da gawarwaki 2,500 da aka binne ba a san ko su waye ba” kuma gawarwakin mutane 1,500 na nan a dakin ajiye gawa.

A cewar rahotannin Majalisar Dinkin Duniya, ‘yan kungiyar M23 dauke da makamai, wadanda ke samun goyon bayan sojojin Rwanda kimanin 4,000, suyka abkawa yankunan, lamarin da ya tilastawa dubban mutane tserewa daga yankin.

A baya-bayan nan ne dakarun M23 suka karbe iko da Bukavu, babban birnin lardin Kivu ta Kudu, bayan da suka kwace Goma, babban birnin lardin Kivu ta Arewa.

Firayim Ministan Kongo ya ce an kashe fiye da mutane 3,000 a Goma kadai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Tabbatar Da Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya
  • Sin Ta Gabatar Da Ka’idar Sarrafa Mutum-Mutumin Inji Mai Kula Da Tsoffi Na Duniya
  • Sin Za Ta Kara Matsa Kaimi Ga Raya Sha’anin Mata Na Duniya
  • Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno
  • Mutum 10 sun mutu a hanyar Damaturu zuwa Maiduguri
  • 40% na matan Kano sun fuskaci cin zarafi a gida —Shugaban Majalisa
  • Iran : Makaman Kare Dangi Na Israila Barazana Ne Ga Zaman Lafiya Da Tsaro
  • Mutum 7,000 Suka Mutu A Rikicin Gabashin Kwango Tun Daga Watan Janairu
  • IRGC : Jana’izar Nasrallah Wani Sakon ‘yan Gwagwarmaya A Duniya Baki Daya