Leadership News Hausa:
2025-04-19@08:39:43 GMT

CMG Ya Kaddamar Da Gasar Basirar Mutum-mutumin Inji Ta Duniya 

Published: 28th, February 2025 GMT

CMG Ya Kaddamar Da Gasar Basirar Mutum-mutumin Inji Ta Duniya 

A ranar 27 ga wata ne babban gidan rediyo da talibijin na kasar Sin na CMG ya kaddamar da gasar basira ta mutum-mutumin inji ta duniya a birnin Beijing.

Babban daraktan CMG Shen Haixiong ya bayyana cewa, masana’antar mutum-mutumin inji ta zama wata muhimmiyar alama ta auna matsayin wata kasa ta fuskar kimiyya da fasahar kere-kere da kuma masana’antar kere-kere na babban mataki.

Kasar Sin ta zama kasa mafi grima a duniya wajen kera mutum-mutumin inji da yin amfani da su. Ta hanyar dogaro da babban dandalin watsa labaru mai karfi, gasar basira ta mutum-mutumin inji ta duniya ta CMG za ta nuna nasarorin da aka samu wajen kera mutum-mutumin inji ta kowane bangare, ta yadda za a hada karfin kimiyya da fasaha da kuma al’adun gargajiya waje guda, ta yadda ainihin kirkire-kirkire da ayyaukan kula da dan Adam za su kyautata tare. Ana sa ran wannan gasa za ta sa kaimi ga ci gaban fasahar mutum-mutumin inji da kuma ba da gudummawa wajen gina kasar Sin mai karfin kimiyya da fasaha da gina al’umma mai makomar bai daya ga bil Adama. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kwararru Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Dangane Da Wayewar Kan Sin Da Afirka 

Gao ya kara da cewa, Sin da kasashen Afirka sun zamo misali na bunkasa hadin gwiwar kasashe masu tasowa, suna kuma gina al’umma mai makomar bai daya ga daukacin bil’adama, kana sun nunawa duniya cewa kasashe masu tasowa na da ikon samar da sabon salon wayewar kan bil’adama na kashin kan su, kuma za su iya bin tafarkin zamanantarwa da ya sabawa na yammacin duniya.

 

A nasa bangare kuwa, daraktan hukumar lura da harkokin waje na kasar Masar Ezzat Saad, cewa ya yi shawarar da Sin ta gabatar ta aiwatar da manufofin zamanantar da duniya, ta samar da karin sassan hadin gwiwarta da kasashen Afirka, tare da yayata kusancin sassan biyu ta fuskar amincewa da juna da hadin gwiwarsu.

 

Saad ya ce, ta hanyar dandaloli irin na wannan taron, sassan biyu sun samu zarafin karfafa alakar al’adu, da ingiza kafuwar kawance na tsawon lokaci bisa tushen cimma moriyar bai daya da kara fahimtar juna. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwararru Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Dangane Da Wayewar Kan Sin Da Afirka 
  • Kasar Sin Ta Nemi Kasashen Duniya Su Taimaka Wa Libya Wajen Fita Daga Kangin Da Take Ciki
  • Amurka Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadancinta Kimani 30 A Duniya
  • Rundunar ‘Yansanda Ta Tuhumi Jami’anta Da ‘Yan Kasar Sin Ke Raba Wa Kudi A Wani Bidiyo Da Ke Yawo
  • Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
  • An Kashe Mutane Fiye Da 300 A Wani Kazamin Fada A Yankin Darfur Da Ke Yammacin Kasar Sudan
  • Iraki Ce Zata Amfana Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka: Inji Sayyed Ammar Hakim
  • WTO Ta Yi Gargadi Akan Karin Kudin Fito Na Amurka
  • Hamas ta bukaci hadin kan duniya domin kawo karshen kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a Gaza
  • Matashi ya kai kansa ofishin ’yan sanda