Leadership News Hausa:
2025-03-30@18:12:09 GMT

An Bude Cibiyar Tattarawa Da Yada Labarai Ta Taruka Biyu Na Sin

Published: 28th, February 2025 GMT

An Bude Cibiyar Tattarawa Da Yada Labarai Ta Taruka Biyu Na Sin

An bude cibiyar tattarawa da yada labarai game da manyan taruka biyu na kasar Sin na shekara-shekara, a otel na Media Center dake birnin Beijing a jiya Alhamis.

Za a kaddamar da taro karo na 3 na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ta 14 ne a ranar 5 ga watan Maris, yayin da za a bude taro na 3 na majalisar bayar da shawarwari kan harkokin siyasa ta kasar Sin ta 14, a ranar 4 ga watan na Maris.

Sama da ‘yan jarida 3,000 ne suka yi rajistar daukar rahotannin tarukan biyu na bana, wanda zai kawo karshen wa’adin tsarin raya kasa karo na 14 da wa’adinsa ya fara daga shekarar 2021 zuwa 2025. Daga cikin ‘yan jaridar, sama da 1,000 sun fito ne daga yankunan Hong Kong da Macao da Taiwan da kuma kasashen waje. Kuma idan aka kwatanta da bara, adadin ‘yan jaridar ya karu a bana.

Cibiyar tattara labaran za ta shirya tarukan manema labarai da wasu shirye-shirye, inda shugabannin sassan gwamnatin tsakiya za su yi jawabai da amsa tambayoyi game da muhimman batutuwa na cikin gida da na kasashen waje. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gobe take Sallah a Nijeriya

An ga jinjirin watan Shawwal a Nijeriya da ke tabbatar da ƙarewar watan azumi na Ramadanan bana.

Ɗaya daga cikin ’yan kwamitin duban wata a Nijeriya (NMSC), Malam Simwal Usman Jibrin ne ya sanar da hakan cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.

Sai dai ya ce ana dakon sanar da ganin jinjirin watan a hukumance daga Majalisar Ƙoli ta Harkokin Addinin Islama a Nijeriya da ke ƙarƙashin jagorancin mai alfarma Sarkin Musulmi.

Hakan ya tabbatar da ƙarewar watan azumi na Ramadanan bana, saboda haka gobe Lahadi take Sallah a Nijeriya.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Kasashen Iran Da Tunisya Suna Shirin Bunkasa Alaka A Fagagen Yawon Bude Ido
  • Kamfanonin Kasashen Waje Na Da Imani Kan Ingancin Kasuwar Kasar Sin 
  • Gobe take Sallah a Nijeriya
  • Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah
  • Sharhi: Taruka Da Gangamin Ranar Quds Ta Duniya 2025
  • An Fitar Da “Takardar Ci Gaban Sha’anin Hakkin Dan Adam A Xizang A Sabon Zamani”
  • Xi Jinping Ya Gana Da Wakilan Masana’antu Da Cinikayya Na Kasa Da Kasa
  • Ɓarayin kekunan ɗinki sun shiga hannu a Borno
  • Kasar Sin Na Adawa Da Kara Yawan Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Amurka Ta Takaita Fitar Da Kayayyakinsu
  • Hainan: An Bude Dandalin Boao Na Asiya Na Bana