HausaTv:
2025-04-19@23:03:04 GMT

Habasha Da Somaliya Sun Cimma Yarjeniyoyin Fahimtar Juna A Tsakaninsu

Published: 28th, February 2025 GMT

A wani mataki na nuna kara kusanci tsakanin kasashen Somaliya da Habasha, shugaban kasar Habasha Abiy Ahmed ya ziyarci Somaliya.

A Shekara guda da ta wuce, kasashen biyu sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna.

Bayan shafe shekara guda ana zaman dar-dar, a watan Disambar da ya gabata ne a kasar Turkiya, kasashen biyu suka sake kulla huldar jakadanci ta hanyar sanya hannu kan yarjejeniyar Ankara.

Shugaban kasar Somaliya Hassan Cheikh Mohamoud ya gabatar a matsayin “mahimmin mataki” na daidaita huldar dake tsakanin kasashen biyu.

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa da aka fitar da yammacin jiya Alhamis, an bayyana cewa: Habasha da Somaliya kasashe ne masu dogaro da juna da makoma guda da kuma ra’ayi daya na tabbatar da zaman lafiya da wadata a yankin.

An tattauna dangantakar diflomasiyya, yaki da kungiyoyin ‘yan ta’adda a yankin, da kuma batutuwan tattalin arziki, musamman sha’awar Habasha na samun damar shiga teku.

A halin da ake ciki dai mahukuntan Somaliyan sun dauki matakin saukaka jigilar kayayyaki daga Habasha zuwa tashar jiragen ruwa na Somaliya, musamman na Berbera dake yankin Somaliland.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Araqchi ya mika rubutaccen sakon Jagora ga Shugaba Putin na Rasha

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya mika rubutacciyar wasikar jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ga shugaban kasar Rasha Vladimir Putin.

Araghchi, wanda ya je birnin Moscow a matsayin shugaban tawagar diflomasiyya don ganawa da wasu manyan jami’an Rasha, ya gana da Putin a yammacin ranar Alhamis.

Ministan ya gabatar da sakon Jagoran ga shugaban kasar Rasha tare da bayyana ra’ayoyi da matsayin Jamhuriyar Musulunci ta Iran dangane da batutuwan da suka shafi ajandar huldar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma ci gaban yanki da sauran batutuwa na kasa da kasa.

Araghchi ya tabo yarjejjeniyar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare da shugaba Putin da takwaransa na Iran, Masoud Pezeshkian suka rattabawa hannu a birnin Moscow a watan Janairu.

Ya kira wannan yarjejeniya a matsayin “aiki mafi mahimmanci ta fuskar hadin gwiwa” tsakanin kasashen biyu, yana mai jaddada aniyar Iran na karfafawa da fadada huldar dake tsakaninta da tarayyar Rasha a dukkan matakai.

Shugaba Putin ya isar da gaisuwa da fatan alheri ga Jagoran juyin juya halin Musulunci tare da jaddada muhimmancin kara karafa  kawance tsakanin Iran da Rasha bisa manyan tsare-tsare.

Ya kara da cewa, karfafa alaka a tsakanin kasashen biyu, tare da hadin gwiwa kan batutuwan da suka shafi gabas ta tsakiya da na kasa da kasa, zai yi amfani da moriyar kasashen biyu, da taimakawa wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Baya ga hakan kuma sun duba sauran batutuwa da suka shafi yakin Ukraine da kuma tattauna batun shawarwari kan nukiliyar Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu  
  • Kwararru Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Dangane Da Wayewar Kan Sin Da Afirka 
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce: Iran Da Saudiyya Za Su Iya Magance Yawancin Matsalolin Yankin Gabas Ta Tsakiya
  • Jagora: Iran a shirye take domin aiki kafada da kafada tare da  Saudiyya
  • Pezeshkian: Hadin gwiwar Iran da Saudiyya zai zama abin koyi ga dukkanin kasashen yankin
  • Araqchi ya mika rubutaccen sakon Jagora ga Shugaba Putin na Rasha
  • Saudiyya da Iran sun jaddada aniyar fadada alakar soji a tsakaninsu
  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Yi Aiki Tare Don Daidaita Mummunan Yanayi A Yankin Manyan Tabkuna Na Afirka
  • Sin Da Malaysia Za Su Samar Sabbin Shekaru 50 Masu Muhimmanci Na Dangantakar Kasashen Biyu
  • Majalisar Kasa Ta Rasha Ta Amince Da Yarjeniyar Dangantaka Ta Musamman Tsakanin Iran Da Kasar