HausaTv:
2025-03-30@19:16:14 GMT

Habasha Da Somaliya Sun Cimma Yarjeniyoyin Fahimtar Juna A Tsakaninsu

Published: 28th, February 2025 GMT

A wani mataki na nuna kara kusanci tsakanin kasashen Somaliya da Habasha, shugaban kasar Habasha Abiy Ahmed ya ziyarci Somaliya.

A Shekara guda da ta wuce, kasashen biyu sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna.

Bayan shafe shekara guda ana zaman dar-dar, a watan Disambar da ya gabata ne a kasar Turkiya, kasashen biyu suka sake kulla huldar jakadanci ta hanyar sanya hannu kan yarjejeniyar Ankara.

Shugaban kasar Somaliya Hassan Cheikh Mohamoud ya gabatar a matsayin “mahimmin mataki” na daidaita huldar dake tsakanin kasashen biyu.

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa da aka fitar da yammacin jiya Alhamis, an bayyana cewa: Habasha da Somaliya kasashe ne masu dogaro da juna da makoma guda da kuma ra’ayi daya na tabbatar da zaman lafiya da wadata a yankin.

An tattauna dangantakar diflomasiyya, yaki da kungiyoyin ‘yan ta’adda a yankin, da kuma batutuwan tattalin arziki, musamman sha’awar Habasha na samun damar shiga teku.

A halin da ake ciki dai mahukuntan Somaliyan sun dauki matakin saukaka jigilar kayayyaki daga Habasha zuwa tashar jiragen ruwa na Somaliya, musamman na Berbera dake yankin Somaliland.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Girgizar ƙasa ta kashe mutum 150 a Myanmar da Thailand

Kimanin mutum 150 ne suka riga mu gidan gaskiya a sanadiyyar wata mummunar girgizar ƙasa daban-daban da suka auku a ƙasashen Myanmar da Thailand.

Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP ya ruwaito cewa girgizar ƙasar wadda ta auku a wannan Juma’ar ta jikkata ɗaruruwan mutane a yayin da baraguzai suka danne gommai.

An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara ’Yan sanda sun haramta hawan Sallah a Kano

Hukumar binciken yanayin ƙasa ta Amurka (USGS) ta bayyana cewa an fuskanci wata mummunar girgizar kasa har kashi biyu masu ƙarfin awo 7.7 da 6.4 a Myanmar, tare kuma da wata girgizar ƙasar mai karfi da ta yi ɓarna a kasar Thailand wacce ta shafi wasu wurare a yankin.

Girgizar ƙasa ta farko ta afku ne a wani wuri mai nisan kilomita 16 a arewa maso yammacin birnin Sagaing wacce ta mamayi aƙalla kilomita 10 da misalin ƙarfe 12:50 na daren ƙasar ranar Juma’a, a cewar hukumar binciken yanayin ƙasar ta Amurka USGS.

Gwamnatin ƙasar da za ta gudanar da bincike kan lamarin cikin gaggawa tare da fara ayyukan ceto da kuma samar da kayayyakin agajin jin kai, kamar yadda ta bayyana a shafinta na Telegram.

A cewar wasu shaidu biyu daga garin Taungnoo da ke yankin Bago da suka zanta da kamfanin dillancin labaru na Reuters, aƙalla mutane uku ne suka mutu bayan wani ɓangare na wani masallaci ya rufta.

Girgizar ƙasar ta yi kaca kaca da cibiyar kasuwancin Bangkok haɗi da tituna da gadoji da kuma wani dogon gini mai hawa 30 da ko kammala shi ba a yi ba.

Tuni dai Firaministan Thailand, Paetongtarn Shinawatra ya ayyana dokar ta ɓaci a Bangkok.

Haka kuma, sojojin da ke mulki a Myanmar sun sanar da ayyana dokar ta ɓaci a babban birnin da kuma birni na biyu mafi girma a ƙasar da wasu jihohi shida.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar
  •  Kasashen Iran Da Tunisya Suna Shirin Bunkasa Alaka A Fagagen Yawon Bude Ido
  • Kamfanonin Kasashen Waje Na Da Imani Kan Ingancin Kasuwar Kasar Sin 
  • Adadin mamata a girgizar kasar Myanmar ya ka 1,644
  • Rikici Ya Turnuke Jam’iyyar SDP A Yayin Da Aka Samu Shugabanni Bangare Biyu A Kogi
  • Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki
  • Girgizar ƙasa ta kashe mutum 150 a Myanmar da Thailand
  • Ɓarayin kekunan ɗinki sun shiga hannu a Borno
  • Kasar Sin Na Adawa Da Kara Yawan Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Amurka Ta Takaita Fitar Da Kayayyakinsu