HausaTv:
2025-02-28@12:27:51 GMT

7 Oktoba : Sojin Isra’ila Sun Amince Da “Cikakkiyar Gazawa” A Harin Hamas

Published: 28th, February 2025 GMT

Rundunar sojin Isra’ila ta amince da “cikakkiyar gazawarta” dangane da harin da kungiyar Hamas ta kai a kudancin kasar a ranar 7 ga watan Oktoba, 2023, wanda ya haifar da yaki a zirin Gaza, bisa sakamakon wani binciken da aka gudanar.

A binciken da sojojin Isra’ila suka yi na cikin gida kan abubuwan da suka faru a ranar 7 ga Oktoba, 2023, jami’an sojin sun amince da cewa sun kasa cika aikinsu a ranar da Hamas ta kai wa Isra’ila hari.

Wani jami’in soji ya shaidawa gidan radiyon RFI cewa sojojin sun “kasa cika aikinsu na kare fararen hula Isra’ila” a harin na ranar 7 ga Oktoba, 2023, yayin da aka fitar da babban sakamakon binciken.

Ya kara da cewa “Fararen hula da dama ne suka mutu a wannan rana kuma suna mamaki ga inda sojojin Isra’ila suke a yayin harin.”

Sojojin sun amince da cewa sun yi kuskure ne game da karfin soja na Hamas, in ji shi.

Baya ga gazawar sojojin Isra’ila, binciken ya yi cikakken bayani kan harin na Hamas da ya yi sanadin mutuwar mutane 1,218 a bangaren Isra’ila, galibi fararen hula, a cewar alkaluman da kamfanin dillancin labarai na AFP ya bayar bisa bayanan hukuma na Isra’ila.

A cewar wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a na baya-bayan nan, kashi 70 cikin 100 na ‘yan Isra’ila suna neman a kafa wata hukumar bincike mai zaman kanta don ba da haske kan wadannan abubuwan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Nebenzia : Hare-haren Sojojin Isra’ila a Lebanon da Syria na kara dagula lamura a yankin

Wakilin kasar Rasha na Majalisar Dinkin Duniya, Vasily Nebenzia ya bayyana cewa, Harin baya-bayan nan da Isra’ila ta kai kan Syria da Lebanon, abubuwa ne da ke kara dagula zaman lafiya a yankin.

A yayin da yake jawabi ga Majalisar Dinkin Duniya, Nebenzia ya ce “daya daga cikin abubuwan da ke nuni da yunkurin dagula zaman lafiya a yankin shi ne yadda Isra’ila ke ci gaba da mamaye yankin Golan na klasar Syria.”

Sauran abubuwan da ke haifar da rashin zaman lafiya, a cewar wakilin Majalisar Dinkin Duniya, su ne yadda “Isra’ila” ke hana ‘yan kasar Lebanon da suka rasa matsugunansu komawa gidajensu a Kudancin kasar, da kuma ayyukan tada hankali da ta yi ta hanyar kai farmakin soji a lokacin jana’izar Sayyed Hassan Nasrallah a wasu yankuna na kudancin kasar ta Lebanon.

Jakadan ya yi Allah wadai da hare-haren da Haramtacciyar Kasar Isra’ila” ta kai a baya-bayan nan a Lebanon da Siriya musamman bayan da Haaretz ta fitar da hotunan tauraron dan adam da ke fallasa shirye-shiryen sojojin mamaya na Isra’ila a kan iyakar Siriya.

Hotunan sun bayyana cewa, Isra’ila ta kafa sabbin sansanonin soji kimanin guda bakawai, tun daga Dutsen Hermon da ke arewacin yankin da ta  kwace tsakanin Siriya da yankunan Falasdinawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kori ma’aikatan Microsoft saboda adawa da yahudawan sahyoniya
  • An Fara Tattaunawa Tsakanin Isra’ila Da Hamas Kan Mataki Na Gaba Na Tsagaita Wuta
  • Boko Haram: An lalata gidaje da makarantu a ƙauyukan Adamawa
  • Isra’ila Ta Saki Fursunonin Falasdinawa Da Dama
  • An Cimma Matsaya Kan Sakin Fursunonin Falasdinawa 206 Da Isra’ila Ta Jinkirta
  • Amurka : Kungiyar DAWN Ta Bukaci ICC Ta Binciki Biden Kan Laifin Hada Kai Da Isra’ila A Laifukan Gaza
  • Hamas ta yi tir da matakin Isra’ila na shirin takura masu ibada a masallacin Quds
  • Nebenzia : Hare-haren Sojojin Isra’ila a Lebanon da Syria na kara dagula lamura a yankin
  • Gwamnatin Kano Ta Amince Juma’a 28 Ga Fabrairu A Matsayin Ranar Hutun Zangon Karatu Na Biyu