HausaTv:
2025-03-30@19:54:03 GMT

7 Oktoba : Sojin Isra’ila Sun Amince Da “Cikakkiyar Gazawa” A Harin Hamas

Published: 28th, February 2025 GMT

Rundunar sojin Isra’ila ta amince da “cikakkiyar gazawarta” dangane da harin da kungiyar Hamas ta kai a kudancin kasar a ranar 7 ga watan Oktoba, 2023, wanda ya haifar da yaki a zirin Gaza, bisa sakamakon wani binciken da aka gudanar.

A binciken da sojojin Isra’ila suka yi na cikin gida kan abubuwan da suka faru a ranar 7 ga Oktoba, 2023, jami’an sojin sun amince da cewa sun kasa cika aikinsu a ranar da Hamas ta kai wa Isra’ila hari.

Wani jami’in soji ya shaidawa gidan radiyon RFI cewa sojojin sun “kasa cika aikinsu na kare fararen hula Isra’ila” a harin na ranar 7 ga Oktoba, 2023, yayin da aka fitar da babban sakamakon binciken.

Ya kara da cewa “Fararen hula da dama ne suka mutu a wannan rana kuma suna mamaki ga inda sojojin Isra’ila suke a yayin harin.”

Sojojin sun amince da cewa sun yi kuskure ne game da karfin soja na Hamas, in ji shi.

Baya ga gazawar sojojin Isra’ila, binciken ya yi cikakken bayani kan harin na Hamas da ya yi sanadin mutuwar mutane 1,218 a bangaren Isra’ila, galibi fararen hula, a cewar alkaluman da kamfanin dillancin labarai na AFP ya bayar bisa bayanan hukuma na Isra’ila.

A cewar wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a na baya-bayan nan, kashi 70 cikin 100 na ‘yan Isra’ila suna neman a kafa wata hukumar bincike mai zaman kanta don ba da haske kan wadannan abubuwan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Iran Ta Yi Allawadai Da Sabon Harin HKI A Kasar Lebanon

Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta bakin kakakinta Dr. Isma’ila Baka’i, ta yi tir da sabbin hare-haren da HKI ta kai wa kasar Lebanon a daidai lokacin da ake bikin ranar Kudus.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na kasar ta Iran ya bayyana cewa; Abinda HKI ta yi keta tsagaita wutar yaki ne,wanda abin a yi tir da shi ne.

Haka nan kuma ya yi ishara da nauyin da ya rataya akan wuyan Majalisar Dinkin Duniya da kuma sauran kasashen da suke cikin sa-ido da ‘yarjeneniyar tsagaita wutar yaki, haka nan kuma ya yi kira zuwa ga kungiyoyin kasa da kasa da su dauki mataki na gaggawa domin kawo karshen maimaita keta tsagaita wutar yaki da ‘yan sahayoniyar suke yi.

Har ila yau, kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya ce; “ Dalilin da ‘yan sahayoniya su ka bijiro da shi na kai wa Lebanon hari,ba zai zama karbabbe ba, don haka wajibi ne ga kungiyoyin kasa da kasa da su dauki matakin yadda ‘yan sahayoniyar suke keta wutar yaki a cikin Gaza, Lebanon da kuma Syria.

Dr. Baka’i ya bayyana abinda HKI take yi da cewa, baraza ce ga zaman lafiya da sulhu na duniya.

Tun bayan tsagaiwa wutar yaki a kasar Lebanon, HKI tana keta ta a duk lokacin da ta so, kamar kuma yadda ta kafa sansanoni biyar da ta girke sojojinta a ciki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar
  • Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wuta
  • Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Hamas A Gaza Ta Amince Da Kafa Gwamnatin Hadin Kan Falasdinawa, Amma Makamanta Jan Layi Ne
  • Hamas ta yi Tir da kakkausar murya da harin Isra’ila kan masu aikin ceto a Gaza
  • Mai Bawa Jagora Shawara Ya Ce ‘Wa’adussadik Na III” Na Kan HKI Na Hanya
  • Kungiyar “White Helmets Ta” A Kasar Siriya Ta Rasha Tallafin Da Take Samu Daga USAID
  •  Iran Ta Yi Allawadai Da Sabon Harin HKI A Kasar Lebanon
  • An kashe mutum 10 a wani sabon hari a Filato
  • An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara