Iran Ta Yi Tir Da Kakkausar Murya Kan Barazanar Soji Da Isra’ila Ke Yi Mata
Published: 28th, February 2025 GMT
Iran ta yi Allah-wadai da kakkausar murya kan barazanar soji da Isra’ila ke yi mata, da kuma sukar da kasashen Yamma suka yi kan karfin tsaron kasar a matsayin rashin hankali da wauta.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Esmaeil Baqaei ya bayyana a jiya Alhamis yayin da jami’an Isra’ila ke ci gaba da yi wa Iran barazanar daukar matakin soji, kasashen yamma na ci gaba da zargin kasar da kara karfin tsaronta.
M. Baqaei ya yi nuni da cewa, yankin yammacin Asiya na fama da wata mamaya da ta dade wacce kamu ta wuce gona da iri da rashin bin doka da oda.
Don haka ya kara da cewa, wajibi ne kawai Iran ta kara karfin tsaronta.
Kalaman nasa sun zo ne bayan ministan harkokin wajen Isra’ila Gideon Saar ya ce ana bukatar daukar matakin soji don dakatar da shirin nukiliyar Iran.
A cikin shekarun da suka gabata, kasashen Yamma sun soki ayyukan Iran a kan shirin nukiliyarta, jirage marasa matuka, tsaron sararin samaniyarta, da kuma shirye-shiryen makamai masu linzaminta, suna masu neman Tehran ta dakatar da su.
Iran ta sha nanata cewa ci gaban da take samu na soji ne kawai don kara kaimi ga kasar kan barazanar abokan gaba, musamman Isra’ila da Amurka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Kasa Ta Rasha Ta Amince Da Yarjeniyar Dangantaka Ta Musamman Tsakanin Iran Da Kasar
Majalisar kasa ta kasar Rasha ta amince da yarjeniyar dangantaka ta musamman tsakanin kasar da JMI a ranar 8 ga watan Afrilun da muke ciki sannan ana saran shugaban kasa Vladimir Putin zai sanyawa yarjeniyar hannu a nan gaba.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa yarjeniyar ta musamman mai kuma dogon zango na shekaru 20 zai bawa kasashen biyu damar tallafawa juna da kuma aiki tare da bangarori daban-daban wadanda suka hada da tsaro makamashi kimiyya da fasaha da sauransu.
Labarin ya kara da cewa idan yarjeniyar ya fara aiki kasashen biyu suna da damar kyautata dangantaka a tsakaninsu, wanda zai rage dogaro da suke yi da kasashen yamma a bangarori da dama.
Dangantakar Tehran da Mosco tana kara karfi ne a dai dai lokacinda al-amuran tsaro suke kara tabarbarewa a yanking abas ta tsakiya. Har’ila yau a dai dai lokacinda kasashen biyu suke fama da takunkuman tattalin arziki mafi muni daga kasashen yamma saboda yaki tsakanin Rasha da Ukraine da kuma shirin makamashin nukliya na kasar Iran da kuma siyasarta a kudancin Asiya.