Aljeriya Ta Yi Watsi Da Barazanar Faransa
Published: 28th, February 2025 GMT
Kasar Aljeriya ta yi watsi da barazanar da kuma wa’adin da kasar faransa ta gindaya ma ta na cewa za ta soke yarjejeniyar da bangarorin biyu suka cimma ta shekarar 1968 wacce ta ba Aljeriya matsayi na musamman.
A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar Aljeriya ta fitar ta ce “A cikin ci gaba da takun tsakar dake wakana (…) Aljeriya ba ta dauki wani mataki ba, kuma ta bar bangaren Faransa da ta matakin da ya dace.
Ita dai Faransa ta yi barazana a ranar Laraba cewa za ta binciki yarjejeniyoyin da ke saukaka yanayin zama, shige da fice da kuma aiki ga ‘yan Aljeriya, dangane da koma bayan da ake samu na tashe-tashen hankula sakamakon wani hari da aka kai a Mulhouse.
Firaministan faransa, François Bayou ya ce kin karbar ‘yan kasar Aljeriya da aka aka kora daga Faransa ba abu ne da ba za a amince da shi ba, wanda a saboda haka ya baiwa Algiers wa’adin makonni 6 domin nuna aniyar ta na yin hadin gwiwa sosai a kan batutuwan da suka shafi bakin haure, inda ya yi barazanar duba yarjejeniyar 1968 dake tsakanin kasashen biyu.
Kasashen faransa da Aljeriya sun shiga tsakun tsaka matuka a baya baya nan musamman kan batun yankin yammacin sahara na ‘yan Polisario da Aljeriya ke goyan baya, wanda faransa ta amince da ikon shi ga kasar Morocco.
Ko a makon nan majalisar al’ummar Aljeriya, kwatankwacin majalisar dattijai ta kasar, ta sanar da cewa ta “dakatar da hulda da majalisar dattawan Faransa, domin nuna adawa da ziyarar da shugabanta Gérard Larcher ya kai a ranakun Litinin da Talata a yankin yammacin Sahara.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gaza : Red Crescent ta yi watsi da rahoton Isra’ila kan kisan da aka yi wa jami’an agaji
Kungiyar agaji ta Red Crescent ta Falasdinu ta yi watsi da rahoton da sojin Isra’ila suka fitar kan kisan da aka yi wa sama da jami’an agajin gaggawa na Gaza a watan da ya gabata, wanda gwamnatin kasar ta ce an kashe ne ta bisa kuskure.
Kungiyar ta yi fatali da rahoton na Isra’ila da cewa ba shi da inganci kuma ba za a amince da shi ba, tana mai jaddada cewa yana cike da karairayi.
A wani rahoto da suka fitar ka abinda ya faru sojojin Isra’ila sun yi ikirarin cewa, an samu ” kura-kurai da yawa” a kisan da akayi wa jami’an agajin a Gaza, suna masu cewa za a kori wani kwamandan sojoji.
“Binciken ya nuna cewa an samu wasu matsaloli na rashin da’a na kwararru, da rashin bin umarni, da kuma gaza yin cikakken bayani kan lamarin,” in ji rundunar.
A ranar 23 ga Maris, ne aka harbe wasu ma’aikatan agaji na Falasdinawa 15 da masu aikin ceto a kusa da Rafah da ke kudancin Gaza.
Sojojin Isra’ila sun sake nanata cewa shida daga cikin likitocin Falasdinawa 15 da Isra’ila ta kashe, ‘yan kungiyar Hamas ne.
Kisan da akayi wa jami’an agajin gaggawa na falasdinu ya fuskanci tofin Allah-tsine daga kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa da dama.
Lamarin dai ya sake fiddo a fili irin ta’asar da Isra’ila ke aikatawa a zirin Gaza.
Da farko dai Isra’ila ta yi ikirarin cewa sun bude wuta ne, saboda yadda motocin suka nufo, a cikin dare, ba fitilu, kuma babu wata masaniya da sojinta suke da a kan zuwan motocin.
Amma kuma daga baya hukumar sojin ta ce, wannan bayani da ta bayar akwai kuskure, bayan da aka gano wani hoton bidiyo a wayar daya daga cikin ma’aikatan agajin da sojin Isra’ilar suka kashe a wannan hari, hoton da ke nuna motocin na tafiya da fitilu a kunne da kuma duk wata alama da za ta fayyace su waye.