HausaTv:
2025-03-30@18:33:18 GMT

Aljeriya Ta Yi Watsi Da Barazanar Faransa

Published: 28th, February 2025 GMT

Kasar Aljeriya ta yi watsi da barazanar da kuma wa’adin da kasar faransa ta gindaya ma ta na cewa za ta soke yarjejeniyar da bangarorin biyu suka cimma ta shekarar 1968 wacce ta ba Aljeriya matsayi na musamman.

A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar Aljeriya ta fitar ta ce “A cikin ci gaba da takun tsakar dake wakana (…) Aljeriya ba ta dauki wani mataki ba, kuma ta bar bangaren Faransa da ta matakin da ya dace.

Ita dai Faransa ta yi barazana a ranar Laraba cewa za ta binciki yarjejeniyoyin da ke saukaka yanayin zama, shige da fice da kuma aiki ga ‘yan Aljeriya, dangane da koma bayan da ake samu na tashe-tashen hankula sakamakon wani hari da aka kai a Mulhouse.

Firaministan faransa, François Bayou ya ce kin karbar ‘yan kasar Aljeriya da aka aka kora daga Faransa ba abu ne da ba za a amince da shi ba, wanda a saboda haka ya baiwa Algiers wa’adin makonni 6 domin nuna aniyar ta na yin hadin gwiwa sosai a kan batutuwan da suka shafi bakin haure, inda ya yi barazanar duba yarjejeniyar 1968 dake tsakanin kasashen biyu.

Kasashen faransa da Aljeriya sun shiga tsakun tsaka matuka a baya baya nan musamman kan batun yankin yammacin sahara na ‘yan Polisario da Aljeriya ke goyan baya, wanda faransa ta amince da ikon shi ga kasar Morocco.

Ko a makon nan majalisar al’ummar Aljeriya, kwatankwacin majalisar dattijai ta kasar, ta sanar da cewa ta “dakatar da hulda da majalisar dattawan Faransa, domin nuna adawa da ziyarar da shugabanta Gérard Larcher ya kai a ranakun Litinin da Talata a yankin yammacin Sahara.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas A Gaza Ta Amince Da Kafa Gwamnatin Hadin Kan Falasdinawa, Amma Makamanta Jan Layi Ne

Kungiyar Hamasa a gaza ta bada sanarwan cewa ta amince da shawarar da kasashen da suke shiga tskaninta da HKI kan cewa ta amince da kafa gwamnatin hadin kan Falasdinawa, amma ba zata taba mika makamanta ga wani ba ko waye shi.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban Kungiyar Khalil Al-Hayya yana fadar haka a jiya Asabar a wani jawabin da ya gabatar da faifen bidiyo.

Al-Hayya ya kara da cewa muna karban dukkan shawarori masu ma’ana idan an bijirosu gare mua. Amma batun makamanmu, ba zamu taba kyale mutanemmu a hannun yahudawan sahyoniyya ko kuma wasu shuwagabannin Falasdinawa wadanda zasu mika su ga yahudawa ba suna ta yawo da hanka;linsu ba.

Yace fatammu ne gwamnatin HKI ba zata hana zabe gudana a kasar Falasdinu da kuma kafa gwamnatin Falasdinawa a gaza da yankin yamma da kogin Jordan sannan birnin Kudus a matsayin babban birnin kasar ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al-Burhan: Sudan Ba Za Ta Shiga Tattaunawa Da RSF Ba
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su
  • ‘Yan Hamayyar Siyasar A Kasar Turkiya Suna Ci Gaba Da Yin Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
  • Hamas A Gaza Ta Amince Da Kafa Gwamnatin Hadin Kan Falasdinawa, Amma Makamanta Jan Layi Ne
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Fiji: Ya Kamata A Koyi Fasahohin Da Kasar Sin Ta Samu A Fannin Raya Kasa
  • Kwamandan IRGC Ya Gargadi Amurka Dangane Da Hari Kan Kasar A Ranar Qudus Ta Duniya
  • Maduro Ya Bayyana Sakataren Harkokin Wajen Amurka Da Cewa Wawa Ne
  • Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba
  • Majalisa ta janye ƙudirin tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma