An Fara Tattaunawa Tsakanin Isra’ila Da Hamas Kan Mataki Na Gaba Na Tsagaita Wuta
Published: 28th, February 2025 GMT
Kasar Masar ta ce an fara tattaunawa tsakanin Isra’ila da Hamas kan mataki na gaba na tsagaita wuta a Gaza.
Ma’aikatar yada labaran kasar Masar ta fada a jiya Alhamis cewa, tawagogin Isra’ila, Qatar da Amurka na birnin Alkahira domin tattaunawa mai zurfi kan yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza.
“Bangarorin da abin ya shafa sun fara tattaunawa mai zurfi don tattaunawa kan matakai na gaba na yarjejeniyar tsagaita wuta, a ci gaba da kokarin tabbatar da aiwatar da fahimtar juna da aka amince da su a baya,” in ji sanarwar.
Ta kara da cewa, masu shiga tsakani suna tattaunawa kan hanyoyin da za a iya “inganta isar da kayayyakin jin kai” zuwa yankin Falasdinu da yaki ya daidaita.
A ranar Alhamis, ministan harkokin wajen Isra’ila Gideon Saar ya ce wata tawaga za ta je Masar domin ganin ko akwai halin tattaunawa kan tsawaita wa’adin zangon farko na tsagaita bude wuta da zai kare nan da kwanaki biyu.
Jami’an gwamnatin sun ce suna neman tsawaita matakin farko, inda Hamas za ta sakin ‘yan Isra’ila guda uku a kowane mako domin musayar Falasdinawa da Isra’ila ke rike da su.
Majalisar ministocin Isra’ila na fuskantar matsin lamba daga jama’a na su tsaya kan tsagaita bude wuta don ‘yantar da sauran fursunonin.
Matakin na farko na tsagaita wutar dai zai kare ne a ranar Asabar.
Kimanin mutane 58 ne Hamas ke tsare da su har yanzu a Gaza, ciki har da 34 da sojojin Isra’ila suka ce sun mutu.
Kungiyar ta Hamas dai ta ce a shirye take ta sako dukkan sauran mutanen da ta ke garkuwa da su gabadaya idan har aka cimma yarjejeniyar a matakin na biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Yi Tir Da Kakkausar Murya Kan Barazanar Soji Da Isra’ila Ke Yi Mata
Iran ta yi Allah-wadai da kakkausar murya kan barazanar soji da Isra’ila ke yi mata, da kuma sukar da kasashen Yamma suka yi kan karfin tsaron kasar a matsayin rashin hankali da wauta.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Esmaeil Baqaei ya bayyana a jiya Alhamis yayin da jami’an Isra’ila ke ci gaba da yi wa Iran barazanar daukar matakin soji, kasashen yamma na ci gaba da zargin kasar da kara karfin tsaronta.
M. Baqaei ya yi nuni da cewa, yankin yammacin Asiya na fama da wata mamaya da ta dade wacce kamu ta wuce gona da iri da rashin bin doka da oda.
Don haka ya kara da cewa, wajibi ne kawai Iran ta kara karfin tsaronta.
Kalaman nasa sun zo ne bayan ministan harkokin wajen Isra’ila Gideon Saar ya ce ana bukatar daukar matakin soji don dakatar da shirin nukiliyar Iran.
A cikin shekarun da suka gabata, kasashen Yamma sun soki ayyukan Iran a kan shirin nukiliyarta, jirage marasa matuka, tsaron sararin samaniyarta, da kuma shirye-shiryen makamai masu linzaminta, suna masu neman Tehran ta dakatar da su.
Iran ta sha nanata cewa ci gaban da take samu na soji ne kawai don kara kaimi ga kasar kan barazanar abokan gaba, musamman Isra’ila da Amurka.