An Fara Tattaunawa Tsakanin Isra’ila Da Hamas Kan Mataki Na Gaba Na Tsagaita Wuta
Published: 28th, February 2025 GMT
Kasar Masar ta ce an fara tattaunawa tsakanin Isra’ila da Hamas kan mataki na gaba na tsagaita wuta a Gaza.
Ma’aikatar yada labaran kasar Masar ta fada a jiya Alhamis cewa, tawagogin Isra’ila, Qatar da Amurka na birnin Alkahira domin tattaunawa mai zurfi kan yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza.
“Bangarorin da abin ya shafa sun fara tattaunawa mai zurfi don tattaunawa kan matakai na gaba na yarjejeniyar tsagaita wuta, a ci gaba da kokarin tabbatar da aiwatar da fahimtar juna da aka amince da su a baya,” in ji sanarwar.
Ta kara da cewa, masu shiga tsakani suna tattaunawa kan hanyoyin da za a iya “inganta isar da kayayyakin jin kai” zuwa yankin Falasdinu da yaki ya daidaita.
A ranar Alhamis, ministan harkokin wajen Isra’ila Gideon Saar ya ce wata tawaga za ta je Masar domin ganin ko akwai halin tattaunawa kan tsawaita wa’adin zangon farko na tsagaita bude wuta da zai kare nan da kwanaki biyu.
Jami’an gwamnatin sun ce suna neman tsawaita matakin farko, inda Hamas za ta sakin ‘yan Isra’ila guda uku a kowane mako domin musayar Falasdinawa da Isra’ila ke rike da su.
Majalisar ministocin Isra’ila na fuskantar matsin lamba daga jama’a na su tsaya kan tsagaita bude wuta don ‘yantar da sauran fursunonin.
Matakin na farko na tsagaita wutar dai zai kare ne a ranar Asabar.
Kimanin mutane 58 ne Hamas ke tsare da su har yanzu a Gaza, ciki har da 34 da sojojin Isra’ila suka ce sun mutu.
Kungiyar ta Hamas dai ta ce a shirye take ta sako dukkan sauran mutanen da ta ke garkuwa da su gabadaya idan har aka cimma yarjejeniyar a matakin na biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An cafke mutum 19 bayan arangama tsakanin sojoji da ’yan shi’a a Abuja
Aƙalla mutum 19 aka kama bayan wata arangama tsakanin mabiya ɗarikar shi’a da jami’an tsaro a Abuja.
Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a a yankin Banex, da ke Wuse 2, inda mutane da dama sun jikkata, sannan mutum ɗaya ya rasu.
An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara Yadda kisan ’yan Arewa 16 a Edo ya tayar da ƙura a faɗin NijeriyaRundunar ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ta ce ’yan shi’a sun kai wa jami’an tsaro hari da bindigogi, duwatsu, da wasu makamai.
A sakamakon haka, aka tura ƙarin dakaru domin kwantar da tarzomar.
“Kwamishinan ’yan sanda, CP Ajao Saka Adewale, ya yi tir da wannan hari da aka kai wa jami’an tsaro,” in ji kakakin rundunar, Josephine Adeh.
“Ana ci gaba da bincike, kuma duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci.”
Wani ganau da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya bayyana yadda rikicin ya ɓarke.
“Ina wucewa kawai sai naga taron jama’a suna jifan jami’an tsaro. Ba zato ba tsammani, sai aka fara jin harbin bindiga, mutane suka fara gudu,” in ji shi.
Jami’an tsaro sun tabbatar da dawowar zaman lafiya a yankin, sannan sun buƙaci jama’a su zauna lafiya tare da bayar da rahoton duk wank abun zargi.