Jigawa Ta Kebe Wuraren 57 don Kare Rikicin Manoma da Makiyaya
Published: 28th, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Jigawa ta ce daga cikin wuraren kiwo guda 400 da ke jihar, ta duba 57 domin dakile rikicin manoma da makiyaya a jihar.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana haka ne a wajen bude taron tuntubar masu ruwa da tsaki kan sauye-sauyen kiwo tare da hadin gwiwa da kwamitin shugaban kasa na aiwatar da gyara harkokin kiwon dabbobi da aka gudanar a Dutse, babban birnin jihar.
Ya ce baya ga samar da tsarin doka na kare wuraren kiwo, manufar za ta kuma tabbatar da amfani da albarkatun kasa mai dorewa a jihar.
Gwamnan ya ce gwamnatin sa ta kuma dauki ma’aikatan kiwon lafiyar dabbobi 300 na al’umma domin su samar da ayyukan ci gaba ga manoma domin inganta harkar noma a jihar.
“Mun dauki aiki tare da horar da ma’aikatan kula da lafiyar dabbobi 300 na al’umma don gudanar da asibitocin kula da dabbobi ta wayar hannu guda 300 a fadin jihar kuma kawo yanzu ra’ayoyin da aka bayar kan hakan ya gamsar da su.
“Mun kuma yi wa dabbobi sama da dubu 560 allurar rigakafi a karkashin shirinmu na rigakafi na yau da kullun, muna ba su kariya daga cututtuka da kuma inganta sana’arsu.
“Wannan matakin ba wai kawai ya inganta kiwon dabbobi ba, har ma ya kara samar da kudin shiga ga manoman mu ta yadda kiyon dabbobi ya dore,” in ji Gwamnan.
Ya yi nuni da cewa ayyukan da gwamnatin jihar ke yi a fannin kiwo na ci gaba da samun sakamako mai kyau a kudurin kawo sauyi da inganta tasirinsa ga tattalin arzikin jihar.
“Yayin da muke shirin samar da ingantaccen tsari mai inganci na Kiwo ga Jiha, abin farin ciki ne a lura cewa ayyukan da muka yi a fannin kiwo sun ci gaba da samun sakamako mai kyau.
Namadi ya jaddada cewa, “Labarin nasarorin da muka samu wajen kafa ginshikin ci gaba mai dorewa sun hada da karfafa hanyoyin ganowa da wuri, da sassautawa da warware rikicin manoma da makiyaya tare da mai da hankali kan wuraren da ake samun matsala a tarihi,” Namadi ya jaddada.
Malam Umar Namadi ya yi alkawarin dorewar hadin gwiwa tsakanin hukumar manoma da makiyaya ta jihar Jigawa da kwamitin tsaro na masu ruwa da tsaki a bangarori da dama domin wanzar da zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya domin dorewar samar da ci gaba a fannin kiwo.
KARSHE/USMAN MZ
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa manoma da makiyaya
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue
Hukumomi a jihar Benue dake Najeriya sun ce adadin wadanda suka mutu a harin da ‘yan bindiga suka kai a hukumomin Ukum da Kogo ya kai 56.
Gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, a wata ziyara a yankin ya shaidawa manema labarai cewa adadin wadanda suka mutu a harin ya kai 56.
”A yanzu, mutum 56 ne suka mutu wadanda ba su ji ba su gani ba, da suka hada da iyaye da maza da mata da kananan yara”, in ji shi.
Gwamnan ya yi kira ga gwamnatin tarayya ta gaggauta daukar matakai domin kawo karshen hare-hare a jihar.
Gwamnan ya ce tuni gwamnatin jihar ta kara tura jami’an tsaro zuwa yankunan domin kwantar da hankula.
Harin na zuwa ne kimanin mako biyu bayan wasu yan bindiga sun kashe fiye da mutum 100 a wasu hare-hare a jihar Plateau mai makwabtaka.