Kebbi Ta Kashe Naira miliyan 67 Wajen Biya Sadakin Ma’aurata 300
Published: 28th, February 2025 GMT
Shugaban jam’iyyar APC na kasa kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ne ya tsaya a matsayin wakilin na angwaye yayin da Mai martaba Sarkin Gwandu, Manjo Janar Muhammad Iliyasu Bashar murabus ne ya tsaya a matsayin wakilin na amaren.
Gwamna Nasir Idris, yayin da yake godewa uwargidansa Hajiya Nafisa Nasir Idris bisa wannan shiri a karkashin gidauniyarta ta “Asusun NANAS ”, ya yi alkawarin bayar da goyon baya da kuma ci gaba da gudanar da shirin na shekara-shekara domin amfanin al’ummar Kebbi, ya kuma shawarci ma’auratan da su kasance masu adalci da mutunta ra’ayin juna.
Ministan Kasafin Kudi da Tsare Tattalin Arziki, Sanata Abubakar Atiku-Bagudu, ya bayyana taron a matsayin tunatarwa ga daidaikun mutane a cikin al’umma da su rika duba kansu tare da tambayar kansu nawa suka taimaka wajen yin aure a yankunansu.
Shima da yake jawabi, sakataren jam’iyyar APC na kasa, Dr Tajuddeen Bashiru, ya lura cewa, ma’auratan ba aure kadai suke yi ba, har ma gwamnatin jihar ta basu karfin gwiwa.
Ya bayyana cewa, gwamnatin jihar Kebbi ba wai kawai ta aurar da ma’aurata 300 ba, amma tana baiwa iyalai 300 damar dogaro da kai.
Gwamnatin jihar Kebbi, ta sauke nauyin da ya rataya a wuyanta na ware naira miliyan 54 na sadakin ma’aurata 300, kayan daki, kayan abinci da duk wani nauyin da ya rataya a wuyan aure in ban da wurin kwana.
Sheik Aminu Ibrahim Daurawa, Sheik Professor Mansur Sokoto, Sheik Professor Mansur Isa da Sheik AbdurRahman Isa-Jega na daga cikin malaman addinin musulunci da suka shaida bikin.
COV/Abdullahi Tukur
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Edo Za Ta Binciki Kisan Matafiya ‘Yan Arewa A Jihar
Sakataren yaɗa labaran gwamnan, Fred Itua, ya bayyana cewa waɗanda aka kashe sun fito daga Fatakwal, a Jihar Ribas, amma ‘yan banga sun ɗauka cewa ‘yan ta’adda ne.
Gwamna Okpebholo ya kai ziyara wajen da lamarin ya faru, inda ya jaddada cewa za a gudanar da bincike mai zurfi domin hukunta masu hannu a kisan.
Amnesty International da tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, sun yi kira da a tabbatar da an yi adalci.
Gwamnan Edo ya yaba wa shugabannin Arewa bisa yadda suka kwantar da hankula tare da guje wa ɗaukar fansa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp