Leadership News Hausa:
2025-03-31@01:00:24 GMT

GORON JUMA’A

Published: 28th, February 2025 GMT

GORON JUMA’A

Sako daga Alawiyya Jilani Jihar Kano:

Ina gaishe da Mummy da Abba, da kannena Zuhra, Sajida, Alhaji, da dukkanin kawayena na islamiyya dana boko wadanda muka kammala dukka, ina gaida Khadija (Sweet Bala), ina gaishe da Siyama Abdul, ina gaishe da Aunty Hajara da sauran ‘yan’uwa da fatan sakon ya iso gare ku kuma da fatan kun yi juma’a lafiya.

Sako daga Balaraba Ibrahim Jihar Kaduna:

Assalam.. Dan Allah a gaishe mun da Sisi ‘yar fucika uwar tsokana, da Hajiya Hazira, da Aunty Amina mai sakwara, ina gaishe da baby nice, da Binta kwaram da sauran wadanda ban gaisar ba wanda suka sanni.

Sako daga Yusuf Uba Muhammad Jihar Kano:

Haj. Rabi’at dan Allah a mikan sakon gaisuwata zuwa ga Baffa Salisu da abokaina kamar su; Zayyanu, Hassan, Fatuhu, Mansur, Aliyu dan ball, su Idris, Shafi’u dake garin Katsina, Alkhairin Allah ya kai masa, sannan ina gaishe da budurwata Maryam Baby, Allah ya sa ta yi juma’a lafiya.

Sako daga Bilyaminu Ahmad Jihar Kaduna:

Sakona zuwa ga dukkanin al’ummar musulmi ne na fadin duniya, ina gaishe da kowa kuma ina yi mana addu’ar fara azumi lafiya mu gama lafiya dan isar Annabi da alkur’ani.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

Sunana Naja’atu Baffa Jihar kaduna:

Ni dai a gaskia ban son akwai wani anko da za ai wannan sallar ko babu ba. Ina son saka takalmi mai dan tudu ba sosai ba, sai mayafi blue black, sai atamfa ta riga (half bubu) da ‘skirt’, sai sarka da dankunne da Awarwaro ‘silver’. Ina sha’awar cin Snacks irinsu meatpie, samosa, doughnut da kuma cake, sai kuma Yoghurt mai inibi. Ina son in ziyarci kanwar babata wacce take a cikin garin Adamawa.

Sunana Aminu Adamu Malam Maduri A Jihar Jigawa:

To batun shidimar sallah sai mu ce Alhamdullilah domin duk tanadin da mutum yayi sai ya kare, duba da yadda kayayyakin suturu ko tufafi suke tsada don haka sai mutum yayi amfani da abun da ya samu, domin gudanar da bikin sallar cikin kwanciyar hankali ya fi komai dadi. To magana ta gaskiya shadda ita ce kalar kayan da zai fi yawa domin ita shadda ba a daina yayinta kuma tana daga cikin kalar suturar da duk mai hali ko sukuni zai so ya dinka, amma wasu kuma za su dinka yaduka domin kowa da irin kalar suturar da ta fi burge shi. To ni dai nafi sha’awar farin kaya musamman yadda manyan kaya ma’ana riga, binjima da wando da kuma hula fara wannan sune kalar suturar dana fi so musamman lokacin zuwa idi. Batun babu zabi duk wanda na samu zan ci, amma nafi son biskin alkama da miyar yakuwa ko jar miya. To da farko dai Masallacin idi shi ne guri na farko, sannan kuma sai ziyarce-ziyarce gidajen ‘Yan’uwa da abokan arziki.

Sunana Zainab Zeey Ilyas Jihar kaduna:

An yi wa sallah tanadi da dama kamar kayan da za a sa, Lalle, kitso, da sauransu. Bana tunanin gaskiya akwai wani anko da aka fitar domin a halin yanzu ko wa abin da Allah ya hore mai zai saka. Ina son saka shadda mai ‘stones’, ina son cin funkaso, tuwon shinkafa da miyar Agushi wadda ta ji ganda, kaji da kayan ciki, sai lemon ginger, sai farfesun zallar naman zabi.

Sunana Anas Bin Malik Achilafia Yankwashi A Jihar Jigawa:

Ana yin tanadi wa bukukuwan Sallah da yawa, amma dai ni kam babu tanadin dana yi wa sallar bana, batun anko  ko yayin kayan da ake siya, ni dai kam har yau ban lura ba, amma dai bana Iyalai na suna sha’awar Shadda, kuma gaskiya ba na ina sha’awar cin sakwara da hadadden lemu (Ubangiji Allah ka kara hore mana). A bisa al’ada kuma muna kaiwa ‘yan’uwa da abokan arzuka ziyara, tare da taya murnar kammala ibada. Ubangiji Allah karva mana ibada, ya sa mun dace.

Sunana Muhammad Isah Zareku Miga A Jihar Jigawa:

Tanadin dana yi wa wannan sallah shi ne ina so ta same ni cikin koshin lafiya da kuma ‘yan canji a cikin aljihuna. Wannan shekarar ta zo da son yin wankan shadda wato shampoo ita ce kowacce saurayi ko budurwa take/yake son sakawa duk da tsadar rayuwa da muke fama da ita. Ina sha’awar saka farar sutura ko shadda da farar hula a lokacin tafiya sallar idi. Abincin da nake muradin ci sh ine funkaso da jar Miya da naman kaji. Ina son kai ziyara zuwa gidan ‘Yan’uwa da abokan arziki in sha Allah.

Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Jihar kano Rano LGA:

Babban tanadi shi ne Allah ya nuna mana ita muna raye da koshin lafiya. Haka ne kam duk da ana cikin yanayi ba za a rasa wadanda suka yin ba amma mu masu iyali iya yaranmu da iyayensu muka samu muka yi wa. da son samune ni dai sabuwar shadda fara idan kuwa ba ita ba to na sami koda koriya ce ko yadi shi ma fari ko koren. Waina da kunun daka ko na alkama da miya. Bayan dawowa daga sallar idi zan je gidan mahaifina da kuma gidan surukaina sai kuma na ‘yan’uwa da abokaina na kusa domin kara sada zumunci. Allah ya karvi ibadunmu.

Sunana Aisha T. Bello Jihar kaduna:

Sallah bikin daya rana in ji masu magana, a gaskiya na yi ma wannan sallah tanadi babba in Allah ya sa muna da rabon gani. Zan sanyaya raina ta samar da abun da na fi so a ci da sha, zan kai ziyara, zan je kallon hawan sallah, sannan zan kikkira ‘yan’uwa domin taya su barka da sallah da yardar Allah. A gaskiya bana jin wannan sallar akwai wani tanadi na anko kamar kullum, duba da yanayin rayuwa ana ta abun ci da sha ne, ina sha’awar saka doguwar riga da salla in sha Allah, sannan in sa babban mayafi in halarci sallar idi. In Allah ya ba ni dama ina so in kai ziyara jihar katsina don ganin dangina da ‘yan’uwa in sha Allah.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Eidl Fitr: Gwamna Dauda Lawal Ya Buƙaci A Samu Haɗin Kai Da Zaman Lafiya
  • Kashe Matafiya: Gwamnatin Kano Ta Aika Tawaga Zuwa Edo
  • Mu Yi Riƙo Da Kyawawan Ɗabi’u Har Bayan Ramadan – Sudais
  • Tawagar Ma’aikatan Ceto Ta Kasar Sin Ta Isa Birnin Yangon Na Kasar Myanmar 
  • Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah
  • Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki
  • Gwamna Abba Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Jarumi Karkuzu
  • Gwamnatin Edo Za Ta Binciki Kisan Matafiya ‘Yan Arewa A Jihar
  • GORON JUMA’A 28-03-2025
  • Ana Gudanar Da Tarukan Ranar Quds Ta Duniya A Wannan Juma’a