Gwamnatin Kano Ta Shirya Taron Bita Don Jami’an Watsa Labarai
Published: 28th, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Kano tare da hadin gwiwar Cibiyar Hulda da Jama’a ta Najeriya (NIPR) sun shirya taron karawa juna sani na tsawon kwanaki uku ga jami’an yada labarai.
Taron na da nufin baiwa Jami’an Watsa Labarai dabarun sadarwa na zamani, tare da mai da hankali kan sabbin hanyoyin inganta sadarwar jama’a a zamani.
Da yake bayyana bude taron, kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya jaddada kudirin gwamnati na ganin sun kware a fannin sadarwa.
Ya jaddada mahimmancin kayan aikin zamani,tare da haɗin gwiwar kafofin watsa labarun, da sadarwa ta hanyar bayanai don tabbatar da ingantaccen kuma da yada bayanai akan lokaci.
Ya kuma bayyana muhimmiyar rawar da Jami’an Watsa Labarai ke takawa wajen tsara fahimtar jama’a, tabbatar da gaskiya, da kuma kiyaye amanar jama’a.
Kwamishinan ya yabawa gwamna Abba Kabir Yusuf bisa amincewa da bayar da tallafin da bayar da horon, inda ya bayyana cewa gwamnati ta bada fifiko wajen bunkasa dan adam a matsayin ginshikin gudanar da shugabanci na gari.
Babban sakataren ma’aikatar, Adamu Bala Muhammad, ya ja hankalin mahalarta taron da su kara yawan wannan dama da kuma amfani da ilimin da suka samu wajen inganta sadarwa da bayar da hidima ga gwamnati.
Shugaban Hukumar NIPR na Jihar Kano, Aliyu Yusuf, ya yabawa gwamnatin jihar bisa daukar nauyin gudanar da taron bitar tare da amincewa da yin rajistar duk jami’an yada labarai na NIPR.
Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, taron ya kunshi kwararrun masu gudanarwa daga hukumar NIPR, wadanda za su karfafa wa mahalarta taron su kara kaimi da dabarun gudanar da ayyukansu.
KHADIJAH ALIYU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Yada Labarai
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Da Saudiyya Sun Tattauna Kan Taron OIC Mai Zuwa
Kasashen Iran da kuma Saudiyya sun tattauna kan halin da ake ciki a yankin dama batun taron kungiyar kasashen Musulmi ta OIC da za’ayi a cikin kwanaki masu zuwa a Jeddah.
Tattaunawar ta wakana ne ta wayar tarho tsakanin ministan harkokin wajen Saudiyya Yarima Faisal bin Farhan da Abass Araghchi, ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran (RII).
A yayin ganawar, bangarorin biyu sun yi nazari kan halin da ake ciki a yankin, tare da tattauna taron ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar OIC da za a yi a Jeddah.
Dama a kwanan baya bangarorin sun tattauna kan shirin shugaban Amurka Donald Trump na kwace zirin Gaza dama tilasta wa falasdinawan yankin kaura zuwa Masar da Jordan, shirin da dukkan kasashen biyu sukayi fatali da shi.
Araghchi ya la’anci shirin na Amurka da ‘yan sahyoniya na tilastawa al’ummar Gaza komawa wasu kasashe a matsayin ci gaba da shirin ‘yan mulkin mallaka na shafe Falasdinu, yana mai jaddada bukatar daukar kwararan matakai na kasashen duniya don tunkarar wannan makirci.
Ya kuma yi kira ga al’ummar musulmi da sauran al’ummar duniya baki daya da su dauki matakin gaggawa kan lamarin.