Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-30@22:13:05 GMT

Gwamnatin Kano Ta Shirya Taron Bita Don Jami’an Watsa Labarai

Published: 28th, February 2025 GMT

Gwamnatin Kano Ta Shirya Taron Bita Don Jami’an Watsa Labarai

Gwamnatin jihar Kano tare da hadin gwiwar Cibiyar Hulda da Jama’a ta Najeriya (NIPR) sun shirya taron karawa juna sani na tsawon kwanaki uku ga jami’an yada labarai.

 

Taron na da nufin baiwa Jami’an Watsa Labarai dabarun sadarwa na zamani, tare da mai da hankali kan sabbin hanyoyin inganta sadarwar jama’a a zamani.

 

Da yake bayyana bude taron, kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya jaddada kudirin gwamnati na ganin sun kware a fannin sadarwa.

 

Ya jaddada mahimmancin kayan aikin zamani,tare da haɗin gwiwar kafofin watsa labarun, da sadarwa ta hanyar bayanai don tabbatar da ingantaccen kuma da yada bayanai akan lokaci.

 

Ya kuma bayyana muhimmiyar rawar da Jami’an Watsa Labarai ke takawa wajen tsara fahimtar jama’a, tabbatar da gaskiya, da kuma kiyaye amanar jama’a.

 

Kwamishinan ya yabawa gwamna Abba Kabir Yusuf bisa amincewa da bayar da tallafin da bayar da horon, inda ya bayyana cewa gwamnati ta bada fifiko wajen bunkasa dan adam a matsayin ginshikin gudanar da shugabanci na gari.

 

Babban sakataren ma’aikatar, Adamu Bala Muhammad, ya ja hankalin mahalarta taron da su kara yawan wannan dama da kuma amfani da ilimin da suka samu wajen inganta sadarwa da bayar da hidima ga gwamnati.

 

Shugaban Hukumar NIPR na Jihar Kano, Aliyu Yusuf, ya yabawa gwamnatin jihar bisa daukar nauyin gudanar da taron bitar tare da amincewa da yin rajistar duk jami’an yada labarai na NIPR.

 

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, taron ya kunshi kwararrun masu gudanarwa daga hukumar NIPR, wadanda za su karfafa wa mahalarta taron su kara kaimi da dabarun gudanar da ayyukansu.

 

KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Yada Labarai

এছাড়াও পড়ুন:

An Fitar Da “Takardar Ci Gaban Sha’anin Hakkin Dan Adam A Xizang A Sabon Zamani”

A yammacin yau Juma’a ne ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gudanar da taron manema labarai a birnin Lhasa na jihar Xizang wato Tibet, inda aka fitar da “Takardar bayanin ci gaban sha’anin kare hakkin dan Adam a Tibet a sabon zamani”.

Takardar ta yi nuni da cewa, a ko da yaushe, jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin da gwamnatin kasar suna mai da hankali kan ayyukan da suka shafi Xizang, kuma suna ci gaba da kyautatawa da raya tsarin mulkin Xizang, da daukar matakai masu inganci don raya tattalin arziki, da kyautata zaman rayuwar jama’a, da kawo alheri ga jama’a, da inganta hadin kai da ci gaban kabilu, da kuma kare hakkin dan Adam na dukkan kabilun jihar Xizang.

Ta kara da cewa, a halin yanzu, jihar Xizang ta samu kwanciyar hankali a bangaren siyasa, da hadin kan kabilu, da bunkasar tattalin arziki da zamantakewar al’umma, lamarin da ya haifar da wani abin al’ajabi na kare hakkin dan Adam a tudun dusar kankara.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano
  • Babu tsamin dangantaka tsakaninmu da Gwamnan Sakkwato — Sarkin Musulmi
  • Kashe Matafiya: Gwamnatin Kano Ta Aika Tawaga Zuwa Edo
  • Rikici Ya Turnuke Jam’iyyar SDP A Yayin Da Aka Samu Shugabanni Bangare Biyu A Kogi
  • Jami’an Tsaro A Jihar Kano Na Tarayyar Najeriya Sun Hana Bikin Dabar NA Sallar Bana
  • Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki
  • An cafke mutum 19 bayan arangama tsakanin sojoji da ’yan shi’a a Abuja
  • An Fitar Da “Takardar Ci Gaban Sha’anin Hakkin Dan Adam A Xizang A Sabon Zamani”
  • Gwamnatin Kaduna Ta Jadadda Kudurin Ta Wajen Samarda Tsaftatacen Ruwan Sha Ga Al’umma 
  • Taron Boao Ya Sake Ba Duniya Damar Ganin Abubuwa Masu Jan Hankali Game Da Sin