HausaTv:
2025-03-31@22:58:35 GMT

Kasashen Habasha da Nijar sun tattauna kan inganta hadin gwiwar soji da tsaro

Published: 28th, February 2025 GMT

Ministar tsaron Habasha Aisha Mohammed ta gana da tawagar sojoji daga Nijar karkashin jagorancin ministan tsaro Salifu Modi, inda bangarorin biyu suka tattauna kan yadda za a inganta hadin gwiwar soja da tsaro.

Ministar tsaron Habasha Aisha Mohammed ta jaddada cewa; Afirka na da karfin fuskantar kalubale ba tare da tsoma bakin waje ba.

A yayin ganawarta da tawagar sojojin kasar Nijar karkashin jagorancin ministan tsaro Salifu Modi a babban birnin kasar Adis Ababa, Mohammed ta jaddada muhimmancin karfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu bisa amincewa da mutunta juna.

Ta sake jaddada aniyar Habasha na tallafawa zaman lafiyar nahiyar da kuma inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen Afirka don fuskantar barazanar tsaro tare.

A nasa bangaren, ministan tsaron Nijar ya jaddada cewa, “Habasha  babbar aminiya ce wajen inganta tsaro da zaman lafiyar yankin.”

Ya kuma bayyana burin kasarsa na cin gajiyar kwarewar kasar Habasha a fannonin horas da sojoji da inganta tsaro.

Bangarorin biyu sun tattauna kan yadda za a inganta hadin gwiwar soji da tsaro, baya ga wasu batutuwa da bangarorin biyu za su ci gajiyar juna.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Jaddada Bukatar Karfafa Cinikayya Da Ketare Tare Da Fadada Bude Kofa

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijar Ta Fice Daga Rundunar Tsaro Ta Haɗin Kai MNJTF
  • Gwamnati Za Ta Inganta Wuraren Tarihi Domin Nishadantarwa A Duk Jihohin Nijeriya 
  • Jakadan Kasar Sin Ya Bukaci Hadin Gwiwar Inganta Amfani Da AI Don Amfanar Da Kowa
  • Nijar ta fice daga rundunar MNJTF mai yaƙi da masu iƙirarin jihadi
  • Kasar Sin Ta Jaddada Bukatar Karfafa Cinikayya Da Ketare Tare Da Fadada Bude Kofa
  • Eid-el-Fitr: Sarkin Kauru Ya Gargadi Masu Bai Wa ‘Yan Ta’adda Bayanai
  •  Kasashen Iran Da Tunisya Suna Shirin Bunkasa Alaka A Fagagen Yawon Bude Ido
  • Sin Da Jamhuriyar Congo Za Su Karfafa Raya Hadin Gwiwar Sin Da Afrika
  • Sin Da Laberiya Sun Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Ta Fuskar Tattalin Arziki Da Fasaha 
  • Adadin mamata a girgizar kasar Myanmar ya ka 1,644