Kasashen Habasha da Nijar sun tattauna kan inganta hadin gwiwar soji da tsaro
Published: 28th, February 2025 GMT
Ministar tsaron Habasha Aisha Mohammed ta gana da tawagar sojoji daga Nijar karkashin jagorancin ministan tsaro Salifu Modi, inda bangarorin biyu suka tattauna kan yadda za a inganta hadin gwiwar soja da tsaro.
Ministar tsaron Habasha Aisha Mohammed ta jaddada cewa; Afirka na da karfin fuskantar kalubale ba tare da tsoma bakin waje ba.
A yayin ganawarta da tawagar sojojin kasar Nijar karkashin jagorancin ministan tsaro Salifu Modi a babban birnin kasar Adis Ababa, Mohammed ta jaddada muhimmancin karfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu bisa amincewa da mutunta juna.
Ta sake jaddada aniyar Habasha na tallafawa zaman lafiyar nahiyar da kuma inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen Afirka don fuskantar barazanar tsaro tare.
A nasa bangaren, ministan tsaron Nijar ya jaddada cewa, “Habasha babbar aminiya ce wajen inganta tsaro da zaman lafiyar yankin.”
Ya kuma bayyana burin kasarsa na cin gajiyar kwarewar kasar Habasha a fannonin horas da sojoji da inganta tsaro.
Bangarorin biyu sun tattauna kan yadda za a inganta hadin gwiwar soji da tsaro, baya ga wasu batutuwa da bangarorin biyu za su ci gajiyar juna.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Manyan jami’an gwamnati sun halarci auren ’yar tsohon Gwamnan Bauchi
Dubban jama’a ne suka hallara domin ɗaurin auren ’yar tsohon Gwamnan Bauchi a Fadar Mai Martaba Sarkin Bauchi ciki har da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima da Ministan Lafiya, Farfesa Mohammed Ali Pate, da Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Yusuf Tuggar.
Cikin baƙi akwai Shugaban Kamfanin rukuin Media trust Malam Kabiru Yusuf da sauran manyan baƙi suka hallara a birnin domin ɗaurin auren da kuma naɗin sarautar “Makama Babba I da aka yi wa tsohon Gwamnan Jihar Bauchi, Mohammed Abdullahi Abubakar.
Masu garkuwa za su mutu ta hanyar rataya a Edo – Okepebolo An tsinci gawar mabaraci mai shekara 75 a NejaAlhaji Bala Ahmad babban limamin Bauchi ne ya jagoranci ɗaurin auren, wanda Shettima ya kasance a matsayin waliyyin ɗiyar tsohon gwamnan yayin da Yusuf Yakubu Wanka, Chigarin Bauchi, ya kasance waliyyin angon, Sadiƙ Mohammed Wanka a wajen ɗaurin auren.
Bayan ɗaurin auren, Sarkin Bauchi, Alhaji Rilwanu Suleimanu Adamu ya naɗa wa tsohon gwamnan rawani a matsayin Makama Babba na farko, sannan ya sa baƙar Alkyabba.
Tun da farko mataimakin shugaban ƙasar, wanda ya sauka a filin jirgin sama na Sa Abubakar Tafawa Balewa ya samu tarba daga gwamnan jihar, Sanata Bala Mohammed da gwamnan Jihar Gombe Mohammed Inuwa Yahaya.
Haka kuma, taron ya samu halartar wasu manyan baƙi da dama, ciki har da tsohon gwamnan jihar Bauchi, Ahmadu Mu’azu, mataimakin gwamnan Yobe, Shugaban Kamfanin Media Trust Malam Kabiru Yusuf da sarakunan gargajiya da jama’a daga kowane fanni.
Fadar Sarkin dai ta cika maƙil a yayin da sauran manyan baƙi daga sassa daban daban su ma suka halarci bikin, inda aka ɗaura auren Sadiƙ Mohammed Wanka, da Khadijatu Mohammed Abdullahi Abubakar akan sadakin Naira 300,000.
A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed ya bayyana godiyarsa ga Shettima, Pate, Tuggar da Gwamnan Jihar Gombe da sauran manyan baƙi bisa halartar ɗaurin auren da kuma bikin naɗin sarautar tsohon Gwamna a matsayin Makama Babba na Bauchi na farko.
Ya kuma taya tsohon Gwamnan murna kan abin da ya bayyana a matsayin mafi kyawu kuma wanda ya cancanta saboda irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban jihar.