An kori ma’aikatan Microsoft saboda adawa da yahudawan sahyoniya
Published: 28th, February 2025 GMT
Kamfanin Microsoft ya kori ma’aikata biyar bayan da suka nuna rashin amincewa da kwangilar da kamfanin ya kulla da sojojin Isra’ila.
A rahoton cibiyar yada labarai ta Falasdinu, ma’aikatan sun gudanar da zanga-zangar ne a hedkwatar Microsoft da ke Redmond a birnin Washington, sanye da riguna masu dauke da taken nuna adawa da amfani da fasahar kamfanin wajen kai wa Falasdinawa hari.
Matakin ya zo ne bayan da aka buga wani rahoto da ke nuna cewa an yi amfani da bayanan sirri na wucin gadi da na’urar tantance gajimare na Microsoft wajen ayyukan sojojin Isra’ila.
Bayan wani bincike da Kamfanin Dillancin Labarai na Associated Press ya yi a baya-bayan nan, ya bayyana cewa kamfanonin fasahar kere-kere na Amurka sun taimaka wa Isra’ila wajen kara yawan laifuka da kashe-kashe a Gaza da Lebanon ta hanyar samar da kayayyakin leken asiri ga gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila.
Jaridar The Guardian ta Burtaniya ta bayar da wani rahoto da ke cewa, Microsoft ya karfafa alakarsa da sojojin Isra’ila tare da ba su tallafin fasaha a yakin Gaza.
Jaridar Guardian ta kara da cewa dogaron da sojojin Isra’ila suka yi kan fasahar Microsoft ya karu matuka a lokacin yakin Gaza, kuma sun yi amfani da hakan wajen aiwatar da kashe-kashe kan Falastinawan Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: sojojin Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Al’umma Sun Nuna Alhininsu Kan Takaddamar Akpabio Da Sanata Natasha
An shawarci majalisar dokokin kasar da su mai da hankali kan ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin kasar nan domin inganta shugabanci nagari.
Masu kiran waya a shirin “KAKAKI” na gidan Rediyon Najeriya Karama FM ne suka bada shawarar hakan a lokacin da suke ba da tasu gudunmawar a kan batutuwan da suka shafi kasa.
Sun bayyana damuwarsu kan rahotannin karar da wata sanata daga jihar Kogi, Natasha Akpoti, ta shigar kan shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, biyo bayan zargin bata suna.
Alhaji Ibrahim Alaramma, Idris Adamu Danfulani, da Sani Batira sun jaddada bukatar shugabannin majalisar su tabbatar da kafa doka mai inganci don yaki da talauci da rashin tsaro.
Shi ma da yake jawabi, wani bako a shirin, Alhaji Suleiman Muhammad ya yi kira ga gwamnati da ta kara samar da ayyukan raya kasa da ababen more rayuwa kamar yadda ake yi a kasashen da suka ci gaba.
Suleiman Kaura