HausaTv:
2025-03-31@01:05:02 GMT

An kori ma’aikatan Microsoft saboda adawa da yahudawan sahyoniya

Published: 28th, February 2025 GMT

Kamfanin Microsoft ya kori ma’aikata biyar bayan da suka nuna rashin amincewa da kwangilar da kamfanin ya kulla da sojojin Isra’ila.

A rahoton cibiyar yada labarai ta Falasdinu, ma’aikatan sun gudanar da zanga-zangar ne a hedkwatar Microsoft da ke Redmond a birnin Washington, sanye da riguna masu dauke da taken nuna adawa da amfani da fasahar kamfanin wajen kai wa Falasdinawa hari.

Matakin ya zo ne bayan da aka buga wani rahoto da ke nuna cewa an yi amfani da bayanan sirri na wucin gadi da na’urar tantance gajimare na Microsoft wajen ayyukan sojojin Isra’ila.

Bayan wani bincike da Kamfanin Dillancin Labarai na Associated Press ya yi a baya-bayan nan, ya bayyana cewa kamfanonin fasahar kere-kere na Amurka sun taimaka wa Isra’ila wajen kara yawan laifuka da kashe-kashe a Gaza da Lebanon ta hanyar samar da kayayyakin leken asiri ga gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila.

Jaridar The Guardian ta Burtaniya ta bayar da wani rahoto da ke cewa,  Microsoft ya karfafa alakarsa da sojojin Isra’ila tare da ba su tallafin fasaha a yakin Gaza.

Jaridar Guardian ta kara da cewa dogaron da sojojin Isra’ila suka yi kan fasahar Microsoft ya karu matuka a lokacin yakin Gaza, kuma sun yi amfani da hakan wajen aiwatar da kashe-kashe kan Falastinawan Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sojojin Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kaduna Ta Jadadda Kudurin Ta Wajen Samarda Tsaftatacen Ruwan Sha Ga Al’umma 

 

Ma’aikatar Ayyuka da Samar da Kayayyakin More Rayuwa, tare da hadin gwiwar First Impression Communication Limited, ta shirya wani taro kan shirin Samar da Ruwa Mai Tsafta a Birane da Karkara da Tsabtace Muhalli da Kiwon Lafiya (SURWASH) da ya gudana a Arewa House, a Kaduna.

 

Da yake bude taron, Kwamishinan Ayyuka da Samar da Kayayyakin More Rayuwa, Dakta Ibrahim Hamza, ya jaddada aniyar gwamnatin jihar na magance matsalar karancin ruwa a jihar.

 

Kwamshinan wanda Mataimakin Daraktan Albarkatun Ruwa, David Roven Aliyu ya wakilta, ya bayyana kokarin da gwamnati ke yi, ciki har da gina rijiyoyin burtsatse a wasu al’ummomi domin inganta tsaftar muhalli da kiwon lafiya.

 

“Shirin SURWASH na Najeriya wani shiri ne da Asusun Bada Lamuni na Duniya (World Bank) ke daukar nauyinsa da dala miliyan 700 domin inganta ayyukan WASH a jihohi bakwai na Najeriya, ciki har da Kaduna.

 

Manufar shirin ita ce samar da ruwan sha mai tsafta ga mutane miliyan shida da kuma inganta tsaftar muhalli ga mutane miliyan 1.4.

Dakta Hamza ya bayyana cewa an ware kananan hukumomi guda shida a Jihar Kaduna wanda suka hada da —Soba, Igabi, Chikun, Jaba, Jema’a, da Sabon Gari—domin tabbatar da su sun samu tsaftatacen Ruwa Sha a yankunan su.

 

“Da zarar wadannan yankuna sun cika ka’idojin da ake bukata, za a kara zabar karin kananan hukumomi guda bakwai domin shirin,” in ji shi.

 

Ya bukaci jama’a su kare kayayyakin tsafta da kiwon lafiya da gwamnati ta samar domin su dade ana amfana da su.

 

A nasa jawabin, Shugaban Shirin SURWASH na Kaduna, Mista Esau Ambinjah, ya jaddada muhimmancin hadin gwiwar al’umma wajen kare rijiyoyin burtsatse da sauran kayayyakin tsafta.

 

Ya kuma bayyana cewa an riga an zabi kananan hukumomi guda bakwai—Sanga, Makarfi, Kudan, Zaria, Kaduna ta Arewa, Kaduna ta Kudu, da Zangon Kataf—domin shirin SURWASH.

 

A nata jawabin, Shugabar Kungiyar Mata Musulmi ta Najeriya (FOMWAN), Amira Hafsatu Musa Isa, ta bada shawarar cewa ya kamata a sanya abun da ya dace da al’adu da addini a cikin shirye-shiryen wayar da kai.

 

Haka kuma, Shugabar Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen mata a Kaduna, Bishop Eister Yawai, ta bukaci a fadada yakin wayar da kan SURWASH zuwa wuraren addinai.

 

Ta bayyana cewa samun tsaftataccen ruwa yana da matukar muhimmanci wajen hana yaduwar cututtukan da ke da nasaba da ruwa.

 

Ta kuma bukaci gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki su kara kaimi wajen magance matsalar karancin ruwa a wasu al’umomi.

 

Wanda ya gabatar da shirin, Yusuf Idris, ya gabatar da sanarwar wayar da kai na SURWASH da aka fassara cikin Hausa da turanci, inda mahalarta suka gabatar da ra’ayoyinsu domin inganta shirin.

 

Cov/Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wuta
  • Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Tawagar Ma’aikatan Ceto Ta Kasar Sin Ta Isa Birnin Yangon Na Kasar Myanmar 
  • Hamas ta yi Tir da kakkausar murya da harin Isra’ila kan masu aikin ceto a Gaza
  • Wani Jami’in Leken Asirin HKI Ya Bukaci Kasashen Afirka Su Taimaka Su Karmi Falasdinawan Da Za;a Kora Daga Gaza
  • Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki
  • Gwamnatin Kaduna Ta Jadadda Kudurin Ta Wajen Samarda Tsaftatacen Ruwan Sha Ga Al’umma 
  • Iran: Ta’addancin sojojin Amurka a kan Yemen ‘barazana’ ne ga zaman lafiyar duniya
  • Tinubu zai sake zama shugaban ƙasa a 2027 — Akpabio