Pezeshkian: Wajibi Ne Kasashen Musulmi Su Kara Karfafa Alakokinsu
Published: 28th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce inganta hadin kai da alaka tsakanin kasashen musulmi da suka hada da Iran da Malaysia na daga cikin abubuwan da ake bukata a halin da ake ciki a duniya.
Pezeshkian ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ta yi da ministan harkokin wajen Malaysia Dato’ Seri Utama Haji Mohamad Bin Haji Hasan a birnin Tehran a wata ziyara da ya kai kasar Iran.
Ya ce a halin yanzu gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila tana aiwatar da abin da take yin a laifuka da wuce gona da iri a yankin saboda kan musuylmi ba hade yake ba.
Ya kara da cewa samar da hadin kai tsakanin jami’ai da ‘yan siyasar kasashen musulmi zai taka muhimmiyar rawa wajen kawar da bambance-bambance, rashin fahimta da talauci a cikin kasashen musulmi.
Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye take domin kara fadada hanyoyin sadarwa da kasashen musulmi ciki har da Malaysia a dukkan fannoni in ji shugaban na Iran.
A ci gaba da jawabin nasa, Pezeshkian ya yi nuni da cewa, an gudanar da taron kwamitin hadin gwiwa na kasashen Iran da Malaysia karo na 8 a birnin Tehran a safiyar Laraba bayan shafe shekaru 17 ana yin irin wannan taro.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen Malaysia ya ce alakar da ke tsakanin Tehran da Kuala Lumpur ta ginu ne bisa fahimta da ‘yan uwantaka.
Ya bayyana aniyar Malaysia na bunkasa alaka da Iran da kuma amfana da karfin Jamhuriyar Musulunci ta fuskar kimiyya, fasaha, ilimi, kayan abinci da noma.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kwararru Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Dangane Da Wayewar Kan Sin Da Afirka
Gao ya kara da cewa, Sin da kasashen Afirka sun zamo misali na bunkasa hadin gwiwar kasashe masu tasowa, suna kuma gina al’umma mai makomar bai daya ga daukacin bil’adama, kana sun nunawa duniya cewa kasashe masu tasowa na da ikon samar da sabon salon wayewar kan bil’adama na kashin kan su, kuma za su iya bin tafarkin zamanantarwa da ya sabawa na yammacin duniya.
A nasa bangare kuwa, daraktan hukumar lura da harkokin waje na kasar Masar Ezzat Saad, cewa ya yi shawarar da Sin ta gabatar ta aiwatar da manufofin zamanantar da duniya, ta samar da karin sassan hadin gwiwarta da kasashen Afirka, tare da yayata kusancin sassan biyu ta fuskar amincewa da juna da hadin gwiwarsu.
Saad ya ce, ta hanyar dandaloli irin na wannan taron, sassan biyu sun samu zarafin karfafa alakar al’adu, da ingiza kafuwar kawance na tsawon lokaci bisa tushen cimma moriyar bai daya da kara fahimtar juna. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp